< Numbers 21 >

1 And when king Arad the Canaanite, who was living toward the south, had heard this, namely, that Israel had arrived by the way of spies, he fought against them. And proving to be the victor, he led away prey from them.
Sa’ad da sarkin Arad, mutumin Kan’ana, wanda yake zaune a Negeb, da ya ji cewa Isra’ila yana zuwa ta hanyar Atarim, sai ya fito, yă yaƙi Isra’ilawa, yă kuma kama waɗansunsu.
2 But Israel, obliging himself by a vow to the Lord, said: “If you deliver this people into my hand, I will wipe away their cities.”
Sai Isra’ila suka yi alkawari wa Ubangiji suka ce, “In ka ba da waɗannan mutane a hannunmu, za mu hallaka dukan garuruwansu ƙaf.”
3 And the Lord heard the prayers of Israel, and he delivered the Canaanite, whom they put to death, overthrowing his cities. And they called the name of that place Hormah, that is, Anathema.
Ubangiji kuwa ya saurari kukan Isra’ila, ya kuma ba da Kan’aniyawa a gare su. Suka hallaka su da biranensu ƙaf; saboda haka aka sa wa wurin suna Horma.
4 Then they set out from mount Hor, by the way that leads to the Red Sea, to circle around the land of Edom. And the people began to tire of their journey and hardships.
Suka kama hanya daga Dutsen Hor ta hanya zuwa Jan Teku, don su kauce wa Edom. Amma mutane suka rasa haƙuri a hanya;
5 And speaking against God and Moses, they said: “Why did you lead us away from Egypt, so as to die in the wilderness? Bread is lacking; there are no waters. Our soul is now nauseous over this very light food.”
suka yi wa Allah da Musa gunaguni, suka ce, “Me ya sa kuka fitar da mu daga Masar, kuka kawo mu mu mutu a wannan hamada? Babu abinci! Babu ruwa! Mu dai mun gaji da wannan abinci marar amfani!”
6 For this reason, the Lord sent fiery serpents among the people, which wounded or killed many of them.
Sai Ubangiji ya aiko da macizai masu dafin a cikinsu, suka sassari mutane, Isra’ilawa masu yawa kuwa suka mutu.
7 And so they went to Moses, and they said: “We have sinned, because we have spoken against the Lord and against you. Pray, so that he may take away these serpents from us.” And Moses prayed for the people.
Mutanen suka zo wurin Musa, suka ce, “Mun yi zunubi, da muka yi wa Ubangiji da kai gunaguni. Ka yi addu’a don Ubangiji yă ɗauke mana macizan nan.” Saboda haka Musa ya yi addu’a domin mutane.
8 And the Lord said to him: “Make a bronze serpent, and place it as a sign. Whoever, having been struck, gazes upon it, shall live.”
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ƙera siffar maciji ka rataye shi a bisa doguwar sanda; kowa da maciji ya sare shi, idan ya dubi macijin nan da ka rataye, zai rayu.”
9 Therefore, Moses made a bronze serpent, and he placed it as a sign. When those who had been struck gazed upon it, they were healed.
Saboda haka Musa ya ƙera macijin tagulla, ya kuma rataye shi bisa doguwar sanda. Sa’an nan duk wanda maciji ya sare shi, ya kuma dubi macijin tagullar, zai warke.
10 And the sons of Israel, setting out, made camp at Oboth.
Isra’ilawa suka kama hanya, suka yi sansani a Obot.
11 Having departed from there, they pitched their tents at Iye-abarim, in the wilderness, which looks out toward Moab, opposite the eastern region.
Sai suka tashi daga Obot, suka yi sansani a Iye Abarim a hamadar da take fuskantar Mowab, wajen fitowar rana.
12 And moving from there, they arrived at the Torrent of Zared.
Daga nan kuma suka ci gaba, suka yi sansani a Kwarin Zered.
13 Having left that place behind, they then made camp opposite Arnon, which is in the desert, and which juts out at the borders of the Amorite. For certainly Arnon is at the limit of Moab, dividing the Moabites and the Amorites.
Suka tashi daga nan, suka sauka kusa da Arnon wanda yake a hamadar da ta miƙe zuwa iyakar Amoriyawa. Arnon shi ne iyakar Mowab, wanda yake tsakanin Mowab da Amoriyawa.
14 About this place, it is said in the book of the wars of the Lord: “As he did at the Red Sea, so will he do at the Torrents of Arnon.”
Shi ya sa Littafin Yaƙoƙin Ubangiji ya ce, “Waheb ta cikin yankin Sufa, da kwaruruka na tuddan Arnon,
15 The stones of the torrents were bent, so that they might rest in Ar and lie back within the borders of the Moabites.
da gangaren kwaruruka, wanda ya nausa zuwa garin Ar, ya kuma dangana da kan iyakar Mowab.”
16 Beyond that place appeared a well, about which the Lord said to Moses: “Gather the people together, and I will give them water.”
Daga can, suka gangara zuwa Beyer, wato, rijiyar da Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattara mutane duka, zan kuwa ba su ruwa.”
17 Then Israel sang this verse: “Let the well rise up.” They sang:
Sai Isra’ilawa suka rera wannan waƙa, “Ki ɓuɓɓugo da ruwa, Ke rijiya! Rera waƙa game da ita,
18 “The well, the leaders dug it, and the commanders of the multitude prepared it, at the direction of the lawgiver, and with their staffs.”
game da rijiyar da’ya’yan sarki suka haƙa, rijiyar da manyan mutane masu sandunan sarauta suka nuna da sandunansu.” Sa’an nan suka tashi daga hamadar, suka tafi Mattana,
19 They went from the wilderness to Mattanah, from Mattanah to Nahaliel, from Nahaliel to Bamoth,
daga Mattana, suka tafi Nahaliyel, daga Nahaliyel, suka tafi Bamot,
20 from Bamoth, a valley in the region of Moab, to the top of Pisgah, which looks out opposite the desert.
daga Bamot kuma suka tafi kwarin da yake cikin Mowab inda ƙwanƙolin Fisga yake fuskantar hamada.
21 Then Israel sent messengers to Sihon, the king of the Amorites, saying:
Isra’ila suka aiki manzanni wurin Sihon sarkin Amoriyawa su ce,
22 “I beg you to permit me to cross through your land. We will not turn aside into the fields or the vineyards. We will not drink waters from the wells. We will travel by the royal way, until we have passed your borders.”
“Ka bari mu ratsa ta ƙasarka. Ba za mu shiga wata gona ba, ba za mu kuma shiga gonar inabi, ko mu sha ruwa daga wata rijiya ba. Za mu bi ta babbar hanyar sarki, har mu fita ƙasarka.”
23 And he was not willing to allow Israel to cross through his borders. But instead, gathering an army, he went out to meet them in the desert, and he arrived at Jahaz and fought against them.
Amma Sihon bai bar Isra’ila su ratsa ta yankinsa ba. Sai ya tara dukan sojojinsa, suka fita zuwa cikin hamada, su yaƙi Isra’ila. Da ya kai Yahaz, sai ya yaƙi Isra’ila.
24 And he was struck down by them with the edge of the sword, and they possessed his land from Arnon, even to Jabbok and the sons of Ammon. For the borders of the Ammonites were held by a strong fortress.
Isra’ila fa suka kashe shi da takobi, suka ƙwace ƙasarsa, tun daga kogin Arnon har zuwa kogin Yabbok, zuwa kan iyakar Ammonawa kawai, gama sun yi wa iyakansu katanga.
25 Therefore, Israel took all his cities and lived in the cities of the Amorite, namely, in Heshbon and its villages.
Isra’ila suka ci dukan biranen Amoriyawa, suka kuma zauna a cikinsu, haɗe da babban birnin Heshbon da dukan ƙauyukanta.
26 Heshbon was the city of Sihon, the king of the Amorites, who fought against the king of Moab. And he took all the land, which had been under his sovereignty, as far as Arnon.
Sihon sarkin Amoriyawa ya yi mulkin Heshbon, bayan ya ci sarkin Mowab na dā da yaƙi, ya kuma ƙwace dukan ƙasarsa har zuwa arewancin kogin Arnon.
27 About this, it is said in the proverb: “Enter into Heshbon. Let the city of Sihon be established and built.
Shi ya sa Amoriyawa suka rubuta wannan waƙa game da Heshbon suka ce, “Ku zo mu sāke gina Heshbon, birnin Sihon.
28 A fire has gone forth from Heshbon, a flame from the town of Sihon, and it has devoured Ar of the Moabites, and the inhabitants of the heights of Arnon.
“Mayaƙansa sun fito kamar harshen wuta suka ƙone birnin Ar na Mowab suna hallaka’yan ƙasar tuddan Arnon.
29 Woe to you, Moab! You are perishing, O people of Chemosh. He gave flight to his sons, and he gave the daughters into captivity, to the king of the Amorites, Sihon.
Kaitonki, Mowab! Gunkinki Kemosh ya yashe mutanenki; aka kuma kama su, aka kai su bauta wajen Sihon sarkin Amoriyawa.
30 Their yoke has been scattered from Heshbon even to Dibon. They have passed through, wearily, into Nophah, and as far as Medeba.”
“Amma mun tumɓuke su, mun hallaka garuruwan Heshbon har zuwa Dibon. Mun ragargaza su har zuwa Nofa wanda ya miƙe zuwa Medeba.”
31 And so Israel lived in the land of the Amorite.
Ta haka Isra’ila suka zauna a ƙasar Amoriyawa.
32 And Moses sent some to explore Jazer. These captured its villages and possessed its inhabitants.
Sai Musa ya aika’yan leƙen asiri zuwa Yazer. Daga baya, sai Isra’ilawa suka ci ƙauyukan da suke kewaye, suka kuma kori Amoriyawa da suke zaune a can.
33 And they turned themselves and ascended, along the way of Bashan. And Og, the king of Bashan, met them with all his people, to fight at Edrei.
Sai suka juya suka haura kan hanya ta zuwa Bashan, inda Og yake sarauta, ya kuwa fito tare da dukan sojojinsa suka yi yaƙi da Isra’ila a Edireyi.
34 And the Lord said to Moses: “Do not be afraid of him. For I have delivered him, and all his people, as well as his land, into your hand. And you shall do to him just as you did to Sihon, the king of the Amorites, the inhabitant of Heshbon.”
Ubangiji ya ce wa Musa, “Kada ka ji tsoronsa, gama na ba da shi a gare ka, da dukan sojojinsa da kuma ƙasarsa. Ka yi da shi yadda ka yi da Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon.”
35 Therefore, they struck him down also, with his sons, and all his people, even to utter destruction, and they possessed his land.
Ta haka suka kashe shi, tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa, ba wanda ya ragu. Suka kuma mamaye ƙasarsa.

< Numbers 21 >