< Numbers 19 >

1 And the Lord spoke to Moses and Aaron, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
2 “This is the ritual that the Lord has appointed for a victim. Instruct the sons of Israel, so that they may bring to you a red cow of full maturity, in which there is no blemish, and which has not carried a yoke.
“Wannan ita ce ƙa’ida wadda Ubangiji ya umarta. Faɗa wa Isra’ilawa su kawo maka jan karsana marar lahani, ko marar aibi wadda ba a taɓa sa ta tă yi noma ba.
3 And you shall deliver it to Eleazar the priest, who, having led it out beyond the camp, shall immolate it in the sight of all.
Ka ba wa Eleyazar firist; a kuma kai ta bayan sansani, a yanka a gaban Eleyazar.
4 And dipping his finger in its blood, he shall sprinkle it seven times, opposite the door of the tabernacle.
Sa’an nan Eleyazar firist zai ɗiba jininta a yatsarsa, yă yayyafa sau bakwai wajen gaban Tentin Sujada.
5 And he shall burn it, while all are watching, delivering into the flame, not only its skin and flesh, but also the blood and dung.
Sa’an nan a ƙone dukan karsanar, haɗe da fatarta, naman, jinin da kayan cikin, yayinda Eleyazar yake kallo.
6 Likewise, cedar wood, and hyssop, and twice-dyed scarlet he shall cast into the flame, by which the cow is consumed.
Firist zai ɗauki itacen al’ul, da hizzob, da jan ulu, yă jefa su a kan karsanar da ake ƙonewa.
7 And then finally, having washed his garments and his body, he shall enter into the camp, and he shall be deeply stained until evening.
Bayan haka, dole firist yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka. Sa’an nan zai iya shiga cikin sansani, amma zai kasance da ƙazanta har yamma.
8 Then he also who had burned it shall wash his garments and his body, and he shall be unclean until evening.
Dole mutumin da ya ƙone ta yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka, shi ma zai kasance da ƙazanta har yamma.
9 Then a clean man shall gather the ashes of the cow, and he shall pour them out beyond the camp, in a very pure place, so that they may be preserved for the multitude of the sons of Israel, and for the water of aspersion, because the cow was burned for sin.
“Mutumin da yake da tsarki, zai tara tokar karsanar, yă sa ta a wurin da yake da tsabta a bayan sansani. Jama’ar Isra’ilawa ne za su adana shi don amfani a ruwan tsabtaccewa; wannan domin tsarkakewa ne daga zunubi.
10 And when he who had carried the ashes of the cow will have washed his garments, he shall be unclean until evening. The sons of Israel, and the newcomers who live among them, shall have this as a holy and perpetual right.
Dole mutumin da ya tara tokar karsanar yă wanke rigunarsa, zai kuwa kasance da ƙazanta har yamma. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta har abada ga Isra’ilawa, da kuma baƙin da suke zama a cikinsu.
11 Whoever touches the corpse of a man, and is, because of this, unclean for seven days,
“Duk wanda ya taɓa gawa, zai kasance da ƙazanta har kwana bakwai.
12 shall be sprinkled from this water on the third and seventh days, and so shall he be cleansed. But if he was not sprinkled on the third day, he is not able to be cleansed on the seventh.
Dole yă tsarkake kansa da ruwa a rana ta uku, da kuma a rana ta bakwai; sa’an nan zai zama da tsarki. Amma in bai tsarkake kansa a rana ta uku da kuma a rana ta bakwai ba, ba zai kasance da tsarki ba.
13 Anyone who will have touched the dead body of a human life, and who has not been sprinkled with this mixture, pollutes the tabernacle of the Lord, and he shall perish out of Israel. For not having been sprinkled with the water of expiation, he shall be unclean, and his filth shall remain upon him.
Duk wanda ya taɓa gawar wani, bai kuma tsarkake kansa ba, ya ƙazantar da tabanakul na Ubangiji ke nan. Dole a ware wannan mutum daga cikin Isra’ilawa. Gama ba a yayyafa ruwan tsabtaccewa a kansa ba; ya ƙazantu, ya kasance da ƙazanta ke nan.
14 This is the law of a man who dies in a tent. All who enter into his tent, and all the vessels which are there, shall be polluted for seven days.
“Ga ƙa’idar da za a bi in mutum ya mutu a cikin tenti. Duk wanda ya shiga tentin, kuma duk wanda yake cikinsa, za su zama da ƙazanta har kwana bakwai,
15 The vessel that has no cover or binding over it shall be unclean.
kuma kowane abin da ake zuba kaya, wanda ba shi da murfi a kansa, zai zama da ƙazanta.
16 If anyone in the field will have touched the corpse of a man, who was killed or who died on his own, or his bone, or his grave, he shall be unclean for seven days.
“Wanda duk yake a fili, ya kuma taɓa gawa wanda aka kashe da takobi, ko wanda ya mutu mutuwar Allah, ko ƙashin mutum, ko kabari, zai ƙazantu har bakwai.
17 And they shall take some of the ashes from the burning and the sin offering, and they shall pour living waters over them into a vessel.
“Ga wanda ya ƙazantu kuwa, a ɗiba toka daga hadaya ta ƙonawa ta tsarkakewa, a zuba a cikin tulu, sa’an nan a zuba ruwa mai gudu a kansu.
18 And into it a man who is clean shall dip hyssop, and he shall sprinkle from it the entire tent, and all its articles, and the men who were polluted by means of contact.
Sa’an nan wanda yake tsarkakakke, zai ɗauki hizzob yă tsoma a ruwa, yă yayyafa a tentin da dukan kayayyakinsa, da kuma a kan mutanen da suke wurin. Dole kuma yă yayyafa ruwan a kan duk wanda ya taɓa ƙashin mutu, ko kabari, ko kuma wanda aka kashe, ko wanda ya yi mutuwa ta Allah.
19 And so, in this manner, what is clean shall purify what is unclean, on the third and seventh days. And having been expiated on the seventh day, he shall wash both himself and his garments, and he shall be unclean until evening.
A rana ta uku, da ta bakwai kuma mai tsarkakewa zai yayyafa wa marar tsarkin ruwa, a rana ta bakwai kuma yă tsarkake shi. Wanda aka tsarkaken kuwa, dole yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka da yamma, zai kuma tsarkaka.
20 If anyone has not been expiated by this ritual, his soul shall perish from the midst of the Church. For he has polluted the Sanctuary of the Lord, and he has not been sprinkled with purifying waters.
Amma in wanda yake da ƙazanta bai tsarkake kansa ba, dole a ware shi daga cikin jama’a, domin ya ƙazantar da wuri mai tsarki na Ubangiji. Ba a yayyafa masa ruwa na tsarkakewa ba, ya zama da ƙazanta.
21 This precept shall be an everlasting ordinance. Likewise, the one who has sprinkled the waters shall wash his garments. All who will have touched the waters of expiation shall be unclean until evening.
Wannan za tă zama musu dawwammamiyar farilla. “Mutumin da ya yayyafa ruwa na tsarkakewa, shi ma dole yă wanke rigarsa. Duk wanda kuma ya taɓa ruwan tsarkakewa, zai kasance da ƙazanta har yamma.
22 Whatever has been touched by something unclean will itself be made unclean. And the soul who touches any of these things shall become unclean until evening.”
Duk abin da mai ƙazanta ya taɓa, ya ƙazantu, kowa kuma ya taɓa wannan abu, ya ƙazantu ke nan, har yamma.”

< Numbers 19 >