< Numbers 14 >

1 And so, crying out, the entire crowd wept throughout that night.
A daren nan, sai dukan jama’ar suka tā da murya, suka yi kuka da ƙarfi.
2 And all the sons of Israel were murmuring against Moses and Aaron, saying:
Dukan Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna, dukan taron kuwa suka ce musu, “Da ma mun mutu a Masar! Ko kuma a wannan hamada ma!
3 “If only we had died in Egypt,” and, “If only we would perish in this vast wilderness,” and, “May the Lord not lead us into this land, lest we fall by the sword, and our wives, as well as our children, be led away as captives. Is it not better to return to Egypt?”
Don me Ubangiji yana kawo mu wannan ƙasa yă bar mu kawai mu mutu da takobi? A kuma kwashe matanmu da’ya’yanmu ganima. Ashe, bai fi mana mu koma Masar ba?”
4 And they said to one another, “Let us appoint our leader, and so return to Egypt.”
Sai suka ce wa junansu, “Mu naɗa wa kanmu shugaba, mu koma Masar.”
5 And when Moses and Aaron heard this, they fell prone on the ground in the sight of the multitude of the sons of Israel.
Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki a gaban jama’ar Isra’ilawa da suka taru a can.
6 Yet truly, Joshua the son of Nun, and Caleb the son of Jephunneh, who themselves had also viewed the land, tore their garments,
Yoshuwa ɗan Nun da Kaleb ɗan Yefunne waɗanda suke tare da masu leƙo asirin ƙasar, suka yayyage tufafinsu
7 and they said to the entire multitude of the sons of Israel: “The land that we circled through is very good.
suka ce wa dukan taron Isra’ilawa, “Ƙasar da muka ratsa, muka kuma leƙi asirinta, tana da kyau sosai.
8 If the Lord will be gracious to us, he will lead us into it, and he will give us the land flowing with milk and honey.
In Ubangiji ya ji daɗinmu, zai kai mu ƙasan nan, ƙasar da take zub da madara da zuma, yă kuwa ba mu ita.
9 Do not choose to be rebellious against the Lord. And do not fear the people of this land, for, like bread, so are we able to devour them. All protection has withdrawn from them. The Lord is with us. Do not be afraid.”
Sai dai kada ku tayar wa Ubangiji. Kada kuma ku ji tsoron mutane ƙasar, domin za mu gama da su. Kāriyarsu ta gama, amma Ubangiji yana nan tare da mu. Kada ku ji tsoronsu.”
10 And when the entire multitude cried out, and they wanted to crush them with stones, the glory of the Lord appeared, over the roof of the covenant, to all the sons of Israel.
Amma taron jama’a suka ce za su jajjefe su da duwatsu. Sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana a Tentin Sujada ga dukan Isra’ilawa.
11 And the Lord said to Moses: “How long will this people disparage me? How long will they refuse to believe me, despite all the signs that I have wrought before them?
Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe mutanen nan za su rena ni? Har yaushe za su ƙi gaskata da ni, duk da yawan mu’ujizan da nake yi a cikinsu?
12 Therefore, I will strike them with a pestilence, and so I will consume them. But you I will make the ruler over a great nation, and one which is mightier than this one.”
Zan buge su duka da annoba, in hallaka su, amma zan mai da kai al’umma mai girma, da kuma ƙarfi fiye da su.”
13 And Moses said to the Lord: “But then the Egyptians, from whose midst you led out this people,
Sai Musa ya ce wa Ubangiji, “Ai, Masarawa za su ji game da wannan! Da ikonka ka fitar da mutanen nan daga cikinsu.
14 and the inhabitants of this land, who have heard that you, O Lord, are among this people, and that you are seen face to face, and that your cloud protects them, and that you go before them with a column of cloud by day, and a column of fire by night,
Za su kuwa gaya wa mutanen wannan ƙasa. Sun riga sun ji cewa kai, ya Ubangiji, kana tare da waɗannan mutane, kuma cewa kai, ya Ubangiji, an gan ka fuska da fuska, cewa girgijenka ya tsaya bisansu, cewa kana tafiya a gabansu cikin ginshiƙin girgije da rana, da ginshiƙin wuta kuma da dare.
15 may hear that you have killed so great a multitude, as if they were one man, and they may say:
In ka kashe dukan mutanen nan gaba ɗaya, al’ummai da suka ji wannan labari game da kai za su ce,
16 ‘He was not able to lead the people into the land about which he had sworn. Therefore, he slew them in the wilderness.’
‘Ubangiji ya kāsa kai waɗannan mutane a ƙasar da ya yi alkawari da rantsuwa ne, shi ya sa ya kashe su a hamada.’
17 Therefore, may the strength of the Lord be magnified, just as you swore, saying:
“Yanzu bari Ubangiji yă nuna ikonsa, kamar dai yadda ka furta.
18 ‘The Lord is patient and full of mercy, taking away iniquity and wickedness, and forsaking no one who is harmless. He visits the sins of the fathers upon the sons, to the third and fourth generation.’
‘Ubangiji mai jinkiri fushi ne, mai yawan ƙauna, mai gafarta zunubi da tawaye. Duk da haka ba ya ƙyale mai laifi, babu horo. Yana horin’ya’ya saboda zunubin iyayensu har tsara ta uku, da ta huɗu.’
19 Forgive, I beg you, the sins of this people, according to the greatness of your mercy, just as you have been gracious to them in their journey from Egypt to this place.”
Bisa ga ƙaunarka mai girma, ka gafarta zunubin mutanen nan, kamar dai yadda ka gafarta musu daga lokacin da suka bar Masar har zuwa yanzu.”
20 And the Lord said: “I have forgiven them according to your word.
Ubangiji ya amsa ya ce, “Na gafarta musu, yadda ka roƙa.
21 Also, as I live, the entire world shall be filled with the glory of the Lord.
Duk da haka, muddin ina raye, kuma muddin ɗaukakar Ubangiji ta cika dukan duniya,
22 And yet, all the men who have seen my majesty, and the signs that I have wrought in Egypt and in the wilderness, and who have tested me ten times already, and yet have not obeyed my voice,
ko ɗaya daga cikinsu da suka ga ɗaukakata da mu’ujizai da na yi a Masar, da kuma a cikin hamada, da suka ƙi yin mini biyayya, suka kuma gwada ni har sau goma,
23 these shall not see the land, about which I swore to their fathers, neither shall any of those who detracted me gaze upon it.
ba ko ɗayansu da zai gan ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa zan ba wa kakanninsu. Ba ko ɗaya da ya rena ni, da zai taɓa ganinta.
24 My servant Caleb, who, being full of another spirit, has followed me, I will lead into this land, through which he has wandered, and his offspring shall possess it.
Amma domin Kaleb bawana ya kasance da ruhu dabam, ya kuma bi ni da zuciya ɗaya, zan kai shi cikin ƙasar da ya je, zuriyarsa kuwa za su gāje ta.
25 For the Amalekites and the Canaanites live in the valleys. Tomorrow, move the camp and return into the wilderness, by the way of the Red Sea.”
Da yake Amalekawa da Kan’aniyawa suna zama a kwarin, gobe sai ka koma baya, ka nufi wajen hamada ta hanyar Jan Teku.”
26 And the Lord spoke to Moses and Aaron, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
27 “How long will this very wicked multitude murmur against me? I have heard the complaints of the sons of Israel.
“Har yaushe wannan muguwar al’umma za tă yi gunaguni a kaina? Na ji koke-koken waɗannan Isra’ilawa masu gunaguni.
28 Therefore, say to them: As I live, says the Lord, as you spoke in my hearing, so will I do to you.
Saboda haka ka gaya musu cewa, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji, zan yi muku daidai da abin da na ji kuke faɗa.
29 In the wilderness, here shall your carcasses lie. All you who were numbered from twenty years and above, and who have murmured against me,
A cikin wannan hamadan, jikunanku za su fāɗi, kowanne a cikinku mai shekara ashirin ko fiye, wanda aka ƙirga shi cikin ƙidaya, wanda kuma ya yi gunaguni a kaina, da zai shiga wannan ƙasa.
30 you shall not enter into the land, over which I lifted up my hand to cause you to live there, except Caleb the son of Jephunneh, and Joshua the son of Nun.
Ba ko ɗaya daga cikinku da zai shiga ƙasar da na ɗaga hannu na rantse, za tă zama gidanku, sai dai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
31 But your little ones, about whom you said that they would be a prey to the enemies, I will lead them in, so that they may see the land that has displeased you.
Amma game da’ya’yanku da kuka ce za a kwashe ganima, zan kawo su cikin ƙasar, su ji daɗin ƙasar wadda kuka ƙi.
32 Your carcasses shall lie in the wilderness.
Amma ku, jikunanku za su fāɗi a wannan hamada.
33 Your sons shall wander in the desert for forty years, and they shall bear your fornication, until the carcasses of their fathers are consumed in the desert.
’Ya’yanku za su zama makiyaya a nan, shekaru arba’in suna shan wahala domin rashin amincinku, har sai mutum na ƙarshe a cikinku ya kwanta a hamada.
34 According to the number of the forty days, during which you examined the land, one year shall be charged for each day. And so, for forty years you shall take back your iniquities, and you shall know my retribution.
Shekaru arba’in, shekara ɗaya a madadi kwana ɗaya cikin kwanakin arba’in da kuka ɗauka kuka leƙi asirin ƙasa, za ku sha wahala saboda zunubanku, ku kuma san abin da ake nufi da sa ni in yi gāba da ku.’
35 For just as I have spoken, so shall I do, to this entire most wicked multitude, which has risen up together against me. In the wilderness, here shall it fade away and die.”
Ni, Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata waɗannan abubuwa a kan dukan muguwar jama’an nan da suka haɗa kai, suka tayar mini. Za su sadu da ƙarshensu a wannan hamada; a nan za su mutu.”
36 Therefore, all the men, whom Moses had sent to contemplate the land, and who, having returned, had caused the entire multitude to murmur against him, disparaging the land as if it were evil,
Saboda haka mutanen da Musa ya aika, su leƙo asirin ƙasar, waɗanda suka komo, suka sa taron jama’a su yi gunaguni a kansa saboda sun kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar,
37 suffered death and were struck down in the sight of the Lord.
waɗannan mutanen da suka kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar, annoba ta buge su, suka kuwa mutu a gaban Ubangiji.
38 But only Joshua the son of Nun, and Caleb the son of Jephunneh remained alive, out of all those who had journeyed to examine the land.
Daga cikin mutanen da suka leƙo asirin ƙasar, Yoshuwa ɗan Nun, da Kaleb ɗan Yefunne ne, kaɗai suka rayu.
39 And Moses spoke all these words to all the sons of Israel, and the people mourned exceedingly.
Da Musa ya gaya wa dukan Isra’ilawa wannan labari, sai suka yi baƙin ciki ƙwarai.
40 And behold, rising up at first light, they climbed to the top of the mountain, and they said, “We are prepared to ascend to the place, about which the Lord has spoken, for we have sinned.”
Kashegari da sassafe suka haura ta wajen ƙasa mai tudu suka ce, “Mun yi zunubi, za mu tafi inda Ubangiji ya yi alkawari.”
41 And Moses said to them: “Why do you transgress the word of the Lord, merely because it will not result in prosperity for you?
Amma Musa ya ce, “Don me kuke rashin biyayya da umarnin Ubangiji? Wannan ba zai yiwu ba!
42 Do not ascend, for the Lord is not with you, lest you be overthrown before your enemies.
Kada ku haura, domin Ubangiji, ba ya tare da ku. Magabtanku za su ci nasara a kanku,
43 The Amalekite and the Canaanite are before you, by whose sword you shall be ruined, for you were not willing to consent to the Lord, and so the Lord is not with you.”
gama Amalekawa da Kan’aniyawa za su kara da ku a can. Domin kun juya daga Ubangiji, ba zai kasance da ku ba, za a kuma karkashe ku da takobi.”
44 But they, having been darkened, ascended to the top of the mountain. But the ark of the testament of the Lord, and Moses, did not withdraw from the camp.
Duk da haka, suka yi tsammani ba zai zama haka ba, sai suka haura ta wajen ƙasa mai tudu, Musa da akwatin alkawarin Ubangiji dai ba su gusa daga sansanin ba.
45 And the Amalekites descended, along with those Canaanites who were living in the mountains. And so, striking and cutting them down, they pursued them all the way to Hormah.
Sai Amalekawa da Kan’aniyawa mazaunan ƙasar tudu, suka gangaro suka auka musu, suka bubbuge su suka kokkore su har Horma.

< Numbers 14 >