< Numbers 11 >

1 Meanwhile, there arose a murmur among the people against the Lord, as if they were grief-stricken because of their labors. And when the Lord had heard it, he was angry. And when the fire of the Lord was enflamed against them, it devoured those who were at the extreme end of the camp.
Da Ubangiji ya ji gunagunin da mutanen suke yi saboda wahalarsu, sai ya husata ƙwarai. Sai wuta daga Ubangiji ta yi ta ci a cikinsu har ta ƙone waɗansu wurare na sansanin.
2 And when the people had cried out to Moses, Moses prayed to the Lord, and the fire was consumed.
Da jama’ar suka yi wa Musa kuka, sai ya yi addu’a ga Ubangiji, wutar kuwa ta mutu.
3 And he called the name of that place, ‘The Burning,’ because the fire of the Lord had burned against them.
Saboda haka aka kira wannan wuri Tabera, gama a wurin ne wuta daga Ubangiji ta ƙuna a cikinsu.
4 So then, the mix of common people, who had ascended with them, were enflamed with desire, and sitting and weeping, with the sons of Israel joining them, they said, “Who will give us flesh to eat?
Wata rana, baƙin da suke cikinsu, suka fara kwaɗayin waɗansu abinci, har suka sa Isra’ilawa suka fara kuka, suna cewa, “Da mun sami nama mun ci mana!
5 We remember the fish that we ate freely in Egypt; we call to mind the cucumbers, and melons, and leeks, and onions, and garlic.
Mun tuna da kifin da muka ci kyauta a Masar, haka ma kayan lambu irin su kukumba, guna, safa, albasa da kuma tafarnuwa.
6 Our life is dry; our eyes look out to see nothing but manna.”
Amma ga shi yanzu ba mu da wani abin marmari; in ba wannan Manna ba!”
7 Now the manna was like coriander seed, but with the color of bdellium.
Manna kuwa kamar tsabar riɗi take, kamanninta kuma kamar ƙaro ne.
8 And the people wandered about, gathering it, and they crushed it with a millstone, or ground it with a mortar; then they boiled it in a pot, and made biscuits out of it, with a taste like bread made with oil.
Mutane sukan fita su tattara ta, su niƙa a dutsen niƙa, ko kuwa su daka a turmi. Su dafa, ko su yi waina da ita. Ɗanɗanonta yakan yi kamar abin da aka yi da man zaitun.
9 And when the dew descended in the night over the camp, the manna descended together with it.
Sa’ad da raɓa tana saukowa da dad dare a kan sansani, Manna ma takan sauko.
10 And so, Moses heard the people weeping by their families, each one at the door of his tent. And the fury of the Lord was greatly enflamed. And to Moses also the matter seemed intolerable.
Musa ya ji mutanen suna ta gunaguni ko’ina a cikin iyalansu, kowane mutum a ƙofar tentinsa. Ubangiji kuwa ya husata ƙwarai, sai Musa ya damu.
11 And so he said to the Lord: “Why have you afflicted your servant? Why do I not find favor before you? And why have you imposed the weight of this entire people upon me?
Sai ya ce wa Ubangiji, “Me ya sa ka kawo wannan damuwar a kan bawanka? Me na yi da ya ɓata maka rai har ka ɗora dukan nauyin mutanen nan a kaina?
12 Could I have conceived this entire multitude, or have given birth to them, so that you might say to me: Carry them in your bosom, as a nursemaid usually carries a little infant, and bring them into the land, about which you have sworn to their fathers?
Ni ne na yi cikin dukan mutanen nan? Ni ne na haife su? To, me ya sa ka ce in ɗauke su a ƙirjina kamar yadda mai reno yake rungume jariri, zuwa ƙasa wadda ka yi alkawari da rantsuwa za ka ba wa kakanninsu?
13 From where would I obtain the flesh to give to so great a multitude? They weep against me, saying, ‘Give us flesh, so that we may eat.’
Ina ne zan sami nama in waɗannan mutane? Sun dinga yin mini kuka suna cewa ‘Ka ba mu nama mu ci!’
14 I alone am unable to sustain this entire people, because it is too heavy for me.
Ba zan iya ɗaukan dukan mutanen nan ni kaɗai ba, nauyin ya yi mini yawa.
15 But if it seems to you otherwise, I beg you to put me to death, and so may I find grace in your eyes, lest I be afflicted with such evils.”
In haka za ka yi da ni, ka kashe ni yanzu, in na sami tagomashi daga gare ka, kada ka bar ni in rayu in ga wannan baƙin ciki.”
16 And the Lord said to Moses: “Gather to me seventy men from the elders of Israel, whom you know to be elders, as well as teachers, of the people. And you shall lead them to the door of the tabernacle of the covenant, and you shall cause them to stand there with you,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattaro mini dattawa saba’in daga cikin mutanen Isra’ila, waɗanda aka sani su ne dattawa da kuma shugabanni a cikin jama’a. Ka sa su zo Tentin Sujada, su tsaya a can tare da kai.
17 so that I may descend and speak to you. And I will take from your spirit, and I will deliver it to them, so that, with you, they may sustain the burden of the people, and so that you will not be weighed down alone.
Zan sauko in yi magana da kai a can, zan kuma ɗauki Ruhun da yake kanka in mai da shi wajensu. Za su taimake ka ɗaukan nauyin mutane, don yă zama ba kai kaɗai ba ne mai ɗaukan kaya.
18 You shall also say to the people: Be sanctified. Tomorrow you will eat flesh. For I have heard you say: ‘Who will give us flesh to eat? It was well with us in Egypt.’ So then, may the Lord give you flesh. And you will eat,
“Ka gaya wa mutane, ‘Ku tsarkake kanku don gobe, za ku ci nama. Ubangiji ya ji ku sa’ad da kuka yi kuka cewa, “Da mun sami nama mun ci mana! Ai, da ba mu da damuwa, gama lokacin da muke zama cikin Masar ba mu da damuwa!” Yanzu Ubangiji zai ba ku nama, za ku kuma ci.
19 not for one day, nor for two, nor for five, nor for ten, nor even for twenty,
Ba za ku ci shi na kwana ɗaya, ko biyu, ko biyar, ko goma, ko kuma kwana ashirin kaɗai ba,
20 but for up to a month of days, until it exits from your nostrils, and until it turns into nausea for you, because you have slipped away from the Lord, who is in your midst, and because you have wept before him, saying: ‘Why did we go forth out of Egypt?’”
amma za ku ci har na wata guda cur, sai ya gundure ku a hanci har ku yi ƙyamarsa, domin kun ƙi Ubangiji wanda yake cikinku, kuka yi kuka a gabansa, kuna cewa, “Don me ma muka bar ƙasar Masar?”’”
21 And Moses said: “There are six hundred thousand footmen of this people, and yet you say, ‘I will give them flesh to eat for a whole month.’
Amma Musa ya ce, “Ga ni a cikin mutane dubu ɗari shida tafe tare da ni, kana kuma cewa, ‘Zan ba su nama su ci har wata guda cur!’
22 Could a multitude of sheep and oxen be slain, so that there would be enough food? Or will the fishes of the sea be gathered together, in order to satisfy them?”
Za su ma sami isashe in har aka yanka musu garkuna tumaki da na shanu? Za su sami isashe in aka kama musu dukan kifin teku?”
23 And the Lord answered him: “Can the hand of the Lord be ineffective? Soon now, you shall see whether my word will be fulfilled in this work.”
Ubangiji ya ce wa Musa, “Akwai abin da ya fi ƙarfina ne? Bari ka gani ko abin da na ce zan yi, zai faru ko babu.”
24 And so, Moses went and explained the words of the Lord to the people. Gathering together seventy men from the elders of Israel, he caused them to stand around the tabernacle.
Saboda haka Musa ya fita ya gaya wa jama’a abin da Ubangiji ya faɗa. Ya tattaro dattawansu saba’in, ya sa suka tsaya kewaye da Tentin Sujada.
25 And the Lord descended in a cloud, and he spoke to him, taking from the Spirit which was in Moses, and giving to the seventy men. And when the Spirit had rested in them, they prophesied; nor did they cease afterwards.
Sa’an nan Ubangiji ya sauko daga girgije, ya yi magana da shi, ya kuma ɗauke Ruhun da yake kan Musa ya ɗora shi a kan dattawa saba’in nan. Sa’ad da Ruhun ya zauna a kansu, sai suka yi annabci, amma daga wannan ba su ƙara yin haka kuma ba.
26 Now there had remained in the camp two of the men, of whom one was called Eldad, and the other Medad, upon whom the Spirit rested; for they also had been enrolled, but they did not go forth to the tabernacle.
To, fa, akwai dattawa biyu da suka kasance a sansani, wato, Eldad da Medad. Su ma an lasafta su cikin dattawan, amma ba su fita zuwa Tentin Sujada ba. Duk da haka Ruhun ya sauka a kansu, suka kuma yi annabci a cikin sansanin.
27 And when they were prophesying in the camp, a boy ran and reported to Moses, saying: “Eldad and Medad prophesy in the camp.”
Wani saurayi ya sheƙa a guje zuwa wajen Musa ya ce, “Eldad da Medad suna can suna annabci a sansani.”
28 Promptly, Joshua the son of Nun, the minister of Moses and chosen from many, said: “My lord Moses, prohibit them.”
Sai Yoshuwa ɗan Nun, wanda yake mataimakin Musa tun yana saurayi, ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, Musa, ka hana su!”
29 But he said, “Why are you jealous on my behalf? Who decides that any of the people may prophesy and that God may give to them his Spirit?”
Amma Musa ya amsa ya ce, “Kana kishi domina ne? Da ma a ce dukan mutanen Ubangiji annabawa ne, da ma a kuma ce Ubangiji ya sa Ruhunsa a kansu mana!”
30 And Moses returned, with those greater by birth of Israel, into the camp.
Sai Musa da dattawan Isra’ila suka koma sansani.
31 Then a wind, going out from the Lord and moving forcefully across the sea, brought quails and cast them into the camp, across a distance of one day’s journey, in every part of the camp all around, and they flew in the air two cubits high above the ground.
Ana nan, sai Ubangiji ya kawo wata iska mai tsanani ta koro makware daga teku. Ta bar su birjik kewaye da sansani, tsayinsu daga ƙasa ya kai kamu biyu, misalin tafiyar nisan yini guda ta kowace fuska.
32 Therefore, the people, rising up, gathered quails all that day and night, and the next day; he who did least well gathered ten homers. And they dried them throughout the camp.
Dukan yini da dukan dare da kuma kashegari, mutane suka fito suka tattara makware. Ba wanda ya kāsa tara ƙasa da garwa goma. Sai suka shanya abinsu kewaye da sansanin.
33 The flesh was still between their teeth, neither had this kind of food ceased, and behold, the fury of the Lord was provoked against the people, and he struck them with an exceedingly great scourge.
Amma da suna cikin cin naman, tun ba su ma haɗiye ba, sai Ubangiji ya husata sosai a kan jama’ar, ya buge su da annoba mai zafi.
34 And that place was called, ‘The Graves of Lust.’ For there, they buried the people who had desired.
Saboda haka aka kira wannan wuri Kibrot Hatta’awa, gama a can ne aka binne mutanen nan makwaɗaita.
35 Then, departing from the Graves of Lust, they arrived in Hazeroth, and they stayed there.
Daga Kibrot Hatta’awa, mutane suka yi tafiya zuwa Hazerot, a can suka sauka.

< Numbers 11 >