< Nehemiah 6 >

1 Now it happened that, when Sanballat, and Tobiah, and Geshem, an Arab, and our other enemies, had heard that I had built the wall, and that there was no interruption remaining in it, (even though, at that time, I had not set up the double doors at the gates, )
Sa’ad da magana ta zo kunnen Sanballat, da Tobiya, da Geshem mutumin Arab da kuma sauran abokan gābanmu cewa na sāke gina katangar har babu sauran tsaguwa da ta ragu, ko da yake har zuwa lokacin ban sa ƙofofi a ƙyamare ba
2 Sanballat and Geshem sent to me, saying: “Come, and let us strike a pact together in the villages, on the plain of Ono.” But they were thinking that they would do me harm.
Sanballat da Geshem suka aika mini wannan saƙo cewa, “Ka zo, mu sadu a wani ƙauye a filin Ono.” Amma makirci ne suke yi don su cuce ni;
3 Therefore, I sent messengers to them, saying: “I am doing a great work, and I cannot descend, lest perhaps it may be neglected when I go out and descend to you.”
saboda haka sai na aika musu da wannan amsa, na ce, “Ina cikin babban aiki, ba zan kuwa iya gangarawa ba. Don me zan bar aikin yă tsaya don in gangara zuwa wurinku?”
4 Then they sent to me, with this same word, four times. And I responded to them with the same word as before.
Suka yi ta aiko mini da wannan saƙo har sau huɗu, ni kuwa na yi ta ba su amsa irin ta dā.
5 And Sanballat sent his servant to me a fifth time, with the former word, and he had a letter in his hand written in this manner:
Sai sau na biya, Sanballat ya aiki mataimakinsa gare ni da irin saƙo guda, kuma a hannunsa akwai wasiƙar da ba a yimƙe ba
6 “It has been heard among the Gentiles, and Geshem has said it, that you and the Jews are planning to rebel, and because of this, you are building the wall and thinking to raise yourself as a king over them. For this reason,
wadda aka rubuta cewa, “An ba da labari cikin al’ummai, kuma Geshem ya ce gaskiya ne, cewa kai da Yahudawa kun shirya tawaye, saboda haka kuke sāke ginin katangar. Ban da haka ma, bisa ga waɗannan rahotanni kana shirin zaman sarkinsu
7 you also have stationed prophets, who preach about you in Jerusalem, saying: ‘There is a king in Judea!’ But the king will hear about these words. Therefore, come now, so that we may go to counsel together.”
har ma ka naɗa annabawa su yi wannan shela game da kai a Urushalima, su ce, ‘Akwai sarki a Yahuda!’ To, wannan rahoto zai koma wurin sarki; saboda haka ka zo, mu tattauna wannan batu.”
8 And I sent to them, saying: “There has been nothing done according to these words, which you have spoken. For you are inventing these things from your own heart.”
Sai na aika masa wannan amsa, na ce, “Babu wani abu haka da yake faruwa; ka dai ƙaga wannan daga tunaninka ne.”
9 For all these men wished to frighten us, thinking that our hands would cease from the work, and that we would cease. For this reason, I strengthened my hands all the more.
Suka dai yi ƙoƙari su tsoratar da mu, suna cewa, “Hannuwansu za su rasa ƙarfin yin aiki, ba kuwa za su ƙare aikin ba.” Amma na yi addu’a na ce, “Yanzu, ya Allah, ka ƙarfafa hannuwana.”
10 And I entered into the house of Shemaiah, the son of Delaiah, the son of Mehetabel, in secret. And he said: “Let us consult together in the house of God, in the midst of the temple. And let us close the doors of the temple. For they will come to kill you, and they will arrive in the night to put you to death.”
Wata rana na tafi gidan Shemahiya ɗan Delahiya, ɗan Mehetabel, wanda aka hana fita a gidansa. Ya ce mini, “Mu sadu gobe a gidan Allah, a cikin haikali, mu kuma kulle ƙofofin haikali, gama mutane suna zuwa su kashe ka, tabbatacce za su zo da dare su kashe ka.”
11 And I said: “How could anyone like me flee? And who like me should enter the temple, so that he may live? I will not enter.”
Amma na ce, “Ya kamata mutum kamar ni yă gudu? Ko kuwa ya kamata wani kamar ni yă shiga cikin haikali don yă ceci ransa? Ba zan tafi ba!”
12 And I understood that God had not sent him, but he had spoken to me as if he were prophesying, and that Tobiah and Sanballat had hired him.
Na gane cewa Allah bai aike shi ba, ya yi annabci a kaina domin Tobiya da Sanballat sun yi hayarsa ne.
13 For he had accepted money, so that I would be afraid, and would sin, and so that they would have some evil with which to rebuke me.
An yi hayarsa don yă sa in ji tsoro in yi zunubi ta yin haka, sa’an nan za su ba ni mugun suna, su wofinta ni.
14 Remember me, O Lord, because of Tobiah and Sanballat, because of their works of this kind. Then, too, Noadiah, a prophetess, and the rest of the prophets, would have made me afraid.
Ya Allahna, ka tuna da Tobiya da Sanballat, saboda abin da suka yi; ka kuma tuna da annabiya Nowadiya da sauran annabawa waɗanda suke ƙoƙari su tsorata ni.
15 Now the wall was completed on the twenty-fifth day of the month of Elul, in fifty-two days.
Cikin kwana hamsin da biyu aka gama gina katangar, a ranar ashirin da biyar ga watan Elul.
16 Then it happened that, when all our enemies had heard of it, all the nations that were around us were afraid, and they were downcast within themselves. For they knew that this work had been accomplished by God.
Sa’ad da dukan abokan gābanmu suka ji haka, dukan al’umman da suke kewaye da mu suka ji tsoro, suka rasa ƙarfin halinsu, domin sun gane cewa wannan aiki an yi shi da taimakon Allahnmu ne.
17 But also, in those days, many letters were being sent by the nobles of the Jews to Tobiah, and were arriving from Tobiah to them.
A waɗannan kwanaki, manyan garin Yahuda suka yi ta aika wasiƙu masu yawa zuwa ga Tobiya, shi kuma ya yi ta aika musu da amsoshi.
18 For there were many in Judea who had sworn an oath to him, because he was the son-in-law of Shecaniah, the son of Arah, and because Jehohanan, his son, had married the daughter of Meshullam, the son of Berechiah.
Gama mutane da yawa a cikin Yahuda sun rantse wa Tobiya za su goyi bayansa, domin ya auri’yar Shekaniya, ɗan Ara. Ɗansa kuma, wato, Yehohanan, ya auri’yar Meshullam, ɗan Berekiya.
19 Moreover, they praised him before me, and they reported my words to him. And Tobiah sent letters, so that he might make me afraid.
Ban da haka ma, mutanen sun yi ta ba ni labarin ayyuka masu kyau da Tobiya ya yi, sa’an nan kuma suna faɗa masa duk abin da na faɗa. Tobiya kuwa ya aika wasiƙu don yă tsorata ni.

< Nehemiah 6 >