< Nehemiah 13 >

1 Now on that day, they read from the book of Moses in the hearing of the people. And in it, there was found written that the Ammonites and the Moabites must not enter the church of God, even for all time,
A wannan rana aka karanta Littafin Musa da ƙarfi a kunnuwan mutane aka kuma sami an rubuta cewa kada a karɓi mutumin Ammon ko mutumin Mowab cikin taron Allah,
2 because they did not meet the sons of Israel with bread and water, and they hired Balaam against them, to curse them. But our God turned the curse into a blessing.
domin ba su taryi Isra’ila da abinci da ruwa ba amma suka yi hayar Bala’am don yă kira la’ana a kansu. (Amma Allahnmu, ya mai da la’anar ta zama albarka.)
3 Now it happened that, when they had heard the law, they separated every foreigner from Israel.
Sa’ad da mutane suka ji wannan doka, sai suka ware daga Isra’ila duk waɗanda suke na baƙon zuriya.
4 And Eliashib, the priest, was over this task; he had been given charge of the treasury of the house of our God, and he was a close relative of Tobiah.
Kafin wannan, an sa Eliyashib firist yă lura da ɗakuna ajiyar gidan Allahnmu. Yana da dangantaka na kurkusa da Tobiya,
5 Then he made for himself a large storeroom, and in that place, there was laid before him gifts, and frankincense, and vessels, and the tithes of grain, wine, and oil, the portions of the Levites, and of the singing men, and of the gatekeepers, and the first-fruits of the priests.
ya kuma tanada masa babban ɗakin da dā ake ajiyar hadayun hatsi da turare da kayayyaki haikali, da kuma zakan hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai da aka umarta don Lawiyawa, mawaƙa da kuma matsaran ƙofofi, da kuma sadakoki domin firistoci.
6 But during all this, I was not in Jerusalem, because in the thirty-second year of Artaxerxes, the king of Babylon, I went to the king, and at the end of some days, I petitioned the king.
Amma yayinda dukan wannan yake faruwa, ba ni a Urushalima, gama a shekara ta talatin da biyu na Artazerzes sarkin Babilon na dawo wurin sarki. A wani lokaci daga baya na nemi izininsa
7 And I went to Jerusalem, and I understood the evil that Eliashib had done for Tobiah, such that he would make him a storeroom in the vestibules of the house of God.
sai na koma zuwa Urushalima. A nan na ji game da mugun abin da Eliyashib ya aikata da ya tanada wa Tobiya ɗaki a filayen gidan Allah.
8 And it seemed to me very evil. And I cast the vessels of the house of Tobiah outside of the storeroom.
Na ɓace rai ƙwarai na kuma zubar da dukan kayan gidan Tobiya daga ɗakin.
9 And I gave instructions, and they cleansed again the storeroom. And I brought back, into that place, the vessels of the house of God, the sacrifice, and the frankincense.
Na umarta a tsarkake ɗakunan, sa’an nan na mayar da kayan gidan Allah a cikin ɗakunan, tare da hadayun hatsi da kuma turare.
10 And I realized that the portions of the Levites had not been given to them, and that each one had fled into his own region, from the Levites, and from the singing men, and from those who were ministering.
Na kuma ji cewa sassan da ake ba wa Lawiyawa ba a ba su ba, cewa kuma dukan Lawiyawa da mawaƙan da suke da hakkin hidima sun koma gonakinsu.
11 And I brought the case before the magistrates, and I said, “Why have we forsaken the house of God?” And I gathered them together, and I caused them to stand at their stations.
Sai na tsawata wa shugabanni na kuma tambaye su na ce, “Me ya sa aka ƙyale gidan Allah?” Sa’an nan na kira su gaba ɗaya na sa su a wuraren aikinsu.
12 And all of Judah brought the tithes of the grain, and the wine, and the oil into the storehouses.
Dukan Yahuda suka kawo zakan hatsi, sabon ruwan inabi da mai cikin ɗakunan ajiya.
13 And we appointed over the storehouses, Shelemiah, the priest, and Zadok, the scribe, and Pedaiah from the Levites, and next to them Hanan, the son of Zaccur, the son of Mattaniah. For they had proven to be faithful. And so the portions of their brothers were entrusted to them.
Na sa Shelemiya firist, Zadok marubuci, da wani Balawe mai suna Fedahiya su lura da ɗakunan ajiya na kuma sa Hanan ɗan Zakkur, ɗan Mattaniya ya zama mataimakinsu, domin an ɗauka waɗannan mutane amintattu ne. Aka ba su hakkin raban kayayyaki wa’yan’uwansu.
14 Remember me, O my God, because of this, and may you not wipe away my acts of compassion, which I have done for the house of my God and for his ceremonies.
Ka tuna da ni saboda wannan, ya Allahna, kuma kada ka shafe abin da na yi da aminci domin gidan Allahna da kuma hidimarsa.
15 In those days, I saw, in Judah, some who were treading the presses on the Sabbath, and who were carrying sheaves, and placing on donkeys burdens of wine, and of grapes, and of figs, and all manner of burdens, and who were bringing these into Jerusalem on the day of the Sabbath. And I contended with them, so that they would sell on a day when it was permitted to sell.
A waɗannan kwanaki, na ga mutane a Yahuda suna matse ruwan inabi a ranar Asabbaci suna kuma kawo hatsi suna labta su a kan jakuna, tare da ruwan inabi,’ya’yan inabi, ɓaure da kaya iri-iri. Suna kuma kawowa dukan wannan cikin Urushalima a ranar Asabbaci. Saboda haka na gargaɗe su a kan sayar da abinci a wannan rana.
16 And some Tyrians dwelt within, who were bringing fish and all kinds of items for sale. And they were selling on the Sabbaths to the sons of Judah in Jerusalem.
Mutane daga Taya waɗanda suke zama a Urushalima suna shigar da kifi da kaya iri-iri na’yan kasuwa suna kuma sayar da su a Urushalima a ranar Asabbaci wa mutanen Yahuda.
17 And I put the nobles of Judah under oath, and I said to them: “What is this evil thing that you are doing, profaning the Sabbath day?
Sai na tsawata wa manyan Yahuda na ce musu, “Wanda irin mugun abu ke nan kuke yi, kuna ƙazantar da ranar Asabbaci?
18 Did not our fathers do these things, and so our God brought all this evil upon us and upon this city? And you are adding more wrath upon Israel by violating the Sabbath!”
Kakanninku ba su yi irin waɗannan abubuwa ba, har Allahnmu ya kawo dukan masifun nan a kanmu da kuma a kan wannan birni? Yanzu kuna tsokanar fushi mai yawa a kan Isra’ila ta wurin ƙazantar da Asabbaci.”
19 And it happened that, when the gates of Jerusalem had rested on the day of the Sabbath, I spoke, and they closed the gates. And I instructed that they should not open them until after the Sabbath. And I appointed some of my servants over the gates, so that no one would carry in a burden on the day of the Sabbath.
Sa’ad da inuwar yamma ya fāɗo a ƙofofin Urushalima kafin Asabbaci, na umarta a rufe ƙofofi kuma kada a buɗe sai Asabbaci ya wuce. Na kafa waɗansu mutanena a ƙofofin don kada a shigo da wani kaya a ranar Asabbaci.
20 And so the merchants and those who sold all kinds of items remained just outside of Jerusalem, once and again.
Sau ɗaya ko biyu,’yan kasuwa da masu sayar da kowane irin kaya suka kwana waje da Urushalima.
21 And I contended with them, and I said to them: “Why are you remaining just beyond the wall? If you do this again, I will send hands upon you.” And so, from that time, they no longer came on the Sabbath.
Amma na ja kunnensu na ce, “Me ya sa kuke kwana kusa da katanga? In kuka ƙara yin haka, zan kama ku.” Daga wannan lokaci har zuwa gaba ba su ƙara zuwa a ranar Asabbaci ba.
22 I also spoke to the Levites, so that they would be cleansed, and would arrive to guard the gates and to sanctify the day of the Sabbath. Because of this also, O my God, remember me and spare me, in accord with the multitude of your mercies.
Sai na umarci Lawiyawa su tsarkake kansu su kuma tafi su yi tsaron ƙofofi don a kiyaye ranar Asabbaci da tsarki. Ka tuna da ni saboda wannan shi ma, ya Allahna, ka nuna mini jinƙai bisa ga madawwamiyar ƙaunarka.
23 But also in those days, I saw some Jews taking wives from the Ashdodites, and the Ammonites, and the Moabites.
Ban da haka, a waɗannan kwanakin na ga mutanen Yahuda waɗanda suka auri mata daga Ashdod, Ammon da Mowab.
24 And their sons spoke partly in the speech of Ashdod, and they did not know how to speak the Jewish language, and they were speaking according to the language of one people or another.
Rabin’ya’yansu suna yaren Ashdod ko kuwa wani yare na waɗansu mutane, ba su kuwa san yadda za su yi Yahudanci ba.
25 And I put them under oath, and I cursed them. And I struck some of their men, and I shaved off their hair, and I made them swear to God that they would not give their daughters to their sons, nor take their daughters for their sons, nor for themselves, saying:
Na tsawata musu na kuma kira la’ana a kansu. Na bugi waɗansu mutane na kuma ja gashin kansu. Na sa suka yi rantsuwa da sunan Allah na ce, “Kada ku ba da’ya’yanku mata aure ga’ya’yansu maza, ba kuwa za ku auri’ya’yansu mata wa’ya’yanku maza ko wa kanku ba.
26 “Did not Solomon, king of Israel, sin in this kind of thing? And certainly, among many nations, there was no king similar to him, and he was beloved of his God, and God set him as king over all of Israel. And yet foreign women led even him into sin!
Ba don aure-aure irin waɗannan ne Solomon sarkin Isra’ila ya yi zunubi ba? A cikin yawancin al’ummai babu sarki kamar sa. Allahnsa ya ƙaunace shi, Allah kuma ya mai da shi sarki a kan dukan Isra’ila, amma duk da haka baren mata suka rinjaye shi ga zunubi.
27 So how could we disobey and do all this great evil, so that we would transgress against our God, and take foreign wives?”
Yanzu za mu ji cewa ku ma kuna yin duk wannan mugunta kuna zama marasa aminci ga Allahnmu ta wurin auren baren mata?”
28 Now one of the sons of Joiada, the son of Eliashib, the high priest, was a son-in-law to Sanballat, a Horonite, and I made him flee from me.
Ɗaya daga cikin’ya’yan Yohiyada maza, ɗan Eliyashib babban firist, surukin Sanballat mutumin Horon ne. Na kuwa kore shi daga wurina.
29 O Lord, my God, remember against those who defile the priesthood and the law of the priests and the Levites!
Ka tuna da su, ya Allahna, domin sun ƙazantar da aikin firist da kuma alkawarin aikin firist da na Lawiyawa.
30 And so I cleansed them from all foreigners, and I established the orders of the priests and the Levites, each one in his ministry.
Saboda haka na tsarkake firistoci da Lawiyawa daga kowane baƙon abu, na kuma ba su aikinsu, kowa ga aikinsa.
31 O my God, remember me also, for good, because of the offering of wood, at the appointed times, and because of the first-fruits. Amen.
Na kuma yi tanadi don sadakokin itace a ƙayyadaddun lokuta, da kuma don nunan fari. Ka tuna da ni da alheri, ya Allahna.

< Nehemiah 13 >