< Nehemiah 10 >

1 And the signatories were: Nehemiah, the cupbearer, the son of Hacaliah, and Zedekiah,
Waɗanda suka buga hatimin su ne, Nehemiya ɗan Hakaliya, wanda yake gwamna. Zedekiya
2 Seraiah, Azariah, Jeremiah,
da Serahiya, da Azariya, da Irmiya,
3 Pashhur, Amariah, Malchijah,
da Fashhur, da Amariya, da Malkiya,
4 Hattush, Shebaniah, Malluch,
da Hattush, da Shebaniya, da Malluk,
5 Harim, Meremoth, Obadiah,
da Harim, da Meremot, da Obadiya,
6 Daniel, Ginnethon, Baruch,
da Daniyel, da Ginneton, da Baruk,
7 Meshullam, Abijah, Mijamin,
da Meshullam, da Abiya, da Miyamin,
8 Maaziah, Bilgai, Shemaiah; these were the priests.
da Ma’aziya, da Bilgai, da kuma Shemahiya. Waɗannan su ne Firistocin.
9 And the Levites were: Jeshua, the son of Azaniah, Binnui of the sons of Henadad, Kadmiel,
Lawiyawan kuwa su ne, Yeshuwa ɗan Azaniya, da Binnuyi ɗan Henadad, da Kadmiyel,
10 and their brothers, Shebaniah, Hodiah, Kelita, Pelaiah, Hanan,
’yan’uwansu kuwa su ne, Shebaniya, da Hodiya, da Kelita, da Felahiya, da Hanan,
11 Mica, Rehob, Hashabiah,
da Mika, da Rehob, da Hashabiya,
12 Zaccur, Sherebiah, Shebaniah,
da Zakkur, da Sherebiya, da Shebaniya,
13 Hodiah, Bani, Beninu.
da Hodiya, da Bani da kuma Beninu.
14 The heads of the people were: Parosh, Pahath-moab, Elam, Zattu, Bani,
Shugabannin mutane su ne, Farosh, da Fahat-Mowab, da Elam, da Zattu, da Bani,
15 Bunni, Azgad, Bebai,
da Bunni, da Azgad, da Bebai,
16 Adonijah, Bigvai, Adin,
da Adoniya, da Bigwai, da Adin,
17 Ater, Hezekiah, Azzur,
da Ater, da Hezekiya, da Azzur,
18 Hodiah, Hashum, Bezai,
da Hodiya, da Hashum, da Bezai,
19 Hariph, Anathoth, Nebai,
da Harif, da Anatot, da Nebai,
20 Magpiash, Meshullam, Hazir,
da Magfiyash, da Meshullam, da Hezir,
21 Meshezabel, Zadok, Jaddua,
da Meshezabel, da Zadok, da Yadduwa
22 Pelatiah, Hanan, Anaiah,
da Felatiya, da Hanan, da Anahiya,
23 Hoshea, Hananiah, Hasshub,
da Hosheya, da Hananiya, da Hasshub,
24 Hallohesh, Pilha, Shobek,
da Hallohesh, da Filha, da Shobek,
25 Rehum, Hashabnah, Maaseiah,
da Rehum, da Hashabna, da Ma’asehiya
26 Ahiah, Hanan, Anan,
da Ahiya, da Hanan, da Anan,
27 Malluch, Harim, Baanah.
da Malluk, da Harim da kuma Ba’ana.
28 And the rest of the people were the priests, the Levites, the gatekeepers, and the singers, the temple servants, and all who had separated themselves, from the peoples of the lands, to the law of God, with their wives, their sons, and their daughters.
“Sauran mutane, wato, firistoci, Lawiyawa, matsaran ƙofofi, mawaƙa, ma’aikatan haikali da dukan waɗanda suka ware kansu daga maƙwabta saboda Dokar Allah, tare da matansu da dukan’ya’yansu maza da mata waɗanda za su iya fahimta,
29 All who were able to understand, pledged on behalf of their brothers, with their nobles, and they came forward to promise and to swear that they would walk in the law of God, which he had given to the hand of Moses, the servant of God, that they would do and keep all the commandments of the Lord our God, and his judgments and his ceremonies,
dukan waɗannan yanzu suka sadu da manyan gari’yan’uwansu, suka rantse, cewa la’ana ta same su idan ba su kiyaye Dokar Allah da aka bayar ta wurin Musa bawan Allah su kuma mai da hankali ga yin biyayya da dukan umarnai, ƙa’idodi da farillan Ubangiji shugabanmu ba.
30 and that we would not give our daughters to the people of the land, and that we would not accept their daughters for our sons,
“Mun yi alkawari ba za mu ba da’ya’yanmu mata aure ga mutanen da suke kewaye da mu ba, ba kuwa za mu auri’ya’yansu mata wa’ya’yanmu maza ba.
31 also that, if the people of the land carry in goods for sale or any useful things, so that they might sell them on the day of the Sabbath, that we would not buy them on the Sabbath, nor on a sanctified day, and that we would release the seventh year and the collection of debt from every hand.
“Sa’ad da maƙwabta suka kawo kayayyaki ko hatsi don su sayar a ranar Asabbaci, ba za mu saya daga gare su a ranar Asabbaci ko a rana mai tsarki ba. Kowace shekarar Asabbaci ba za mu nome ƙasa ba kuma za mu yafe kowane irin bashi.
32 And we established precepts over ourselves, so that we would give one third part of a shekel each year for the work of the house of our God,
“Mun ɗauka hakkin bin umarnai na ba da kashi ɗaya bisa uku na shekel kowace shekara don hidimar gidan Allahnmu.
33 for the bread of the presence, and for the continual sacrifice, and for a continual holocaust on the Sabbaths, on the new moons, on the solemnities, and for the holy things, and for the sin offering, so that atonement would be made for Israel, and for every use within the house of our God.
Za mu tanada burodin da ake ajiye a kan tebur; za mu ba da hadayun hatsi da hadayun ƙonawa na kullum; za mu ba da hadayun Asabbatai, da na bukukkuwan Sabon Wata da na bukukkuwan da aka ƙayyade; za mu ba da hadayu masu tsarki; za mu ba da hadayun zunubi don a yi kafara domin Isra’ila; mu kuma ba da abubuwan da ake bukata dukan domin ayyukan gidan Allahnmu.
34 Then we cast lots concerning the oblation of the wood among the priests, and the Levites, and the people, so that it would be carried into the house of our God, by the households of our fathers, at set times, from the times of one year to another, so that they might burn upon the altar of the Lord our God, just as it was written in the law of Moses,
“Mu, firistoci, da Lawiyawa da kuma mutane, mun jefa ƙuri’a don a san lokacin da kowane iyalinmu zai kawo sadakar itace don ƙonewa a gidan Allahnmu a ƙayyadaddun lokuta a bagaden Ubangiji Allahnmu, kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka.
35 and so that we might bring in the first-fruits of our land, and the first-fruits of all the produce from every tree, from year to year, in the house of our Lord,
“Mun kuma ɗauka hakkin kawo nunan fari na hatsinmu da kuma na kowane itace mai ba da’ya’ya a gidan Ubangiji kowace shekara.
36 and the firstborn of our sons, and of our cattle, just as it was written in the law, and the firstborn of our oxen and our sheep, so that they might be offered in the house of our God, to the priests who minister in the house of our God,
“Kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka, za mu kawo ɗan fari na’ya’yanmu maza da na garken shanunmu, da na tumakinmu, da kuma na awakinmu a gidan Allahnmu, don firistocin da suke aikin a can.
37 and so that we might bring in the first-fruits of our foods, and of our libations, and the fruits of every tree, also of the vintage and of the oil, to the priests, to the storehouse of our God, with the tithes of our land for the Levites. The Levites also shall receive tithes from our works out of all the cities.
“Ban da haka ma, za mu kawo wa ɗakunan ajiyar gidan Allahnmu, abincinmu na farko daga ƙasa, na hadayun hatsinmu, na’ya’yan dukan itatuwanmu da kuma na sabon ruwan inabinmu da mai namu wa firistoci. Za mu kuma kawo zakkar hatsinmu wa Lawiyawa, gama Lawiyawa ne ke karɓan Zakka cikin dukan garuruwan da muke noma.
38 Now the priest, the son of Aaron, shall be with the Levites in the tithes of the Levites, and the Levites shall offer a tenth part of their tithes in the house of our God, to the storeroom in the house of the treasury.
Firist wanda yake daga zuriyar Haruna zai raka Lawiyawa sa’ad da suke karɓan zakka, Lawiyawan kuma za su kawo kashi ɗaya bisa goma na zakka zuwa gidan Allahnmu, su kawo a ɗakunan ajiya na baitulmali.
39 For the sons of Israel and the sons of Levi shall carry to the storehouse the first-fruits of the grain, of the wine, and of the oil. And the sanctified vessels shall be there, and the priests, and the singing men, and the gatekeepers, and the ministers. And we shall not forsake the house of our God.
Mutanen Isra’ila haɗe da Lawiyawa, za su kawo sadakokinsu na hatsi, sabon ruwan inabi da mai a ɗakunan ajiya inda ake ajiyar kayayyakin wuri mai tsarki da kuma inda firistoci, matsaran ƙofofi da kuma mawaƙa suke zama. “Ba za mu ƙyale gidan Allahnmu ba.”

< Nehemiah 10 >