< Micah 5 >

1 Now you will be devastated, you daughter of a robber. They have placed a blockade against us, with a rod they will strike the jaw of the judge of Israel.
Ki tattara sojojinki, ya ke birnin mayaƙa, gama an kewaye mu da yaƙi. Za su bugi kumatun mai mulkin Isra’ila da sandar ƙarfe.
2 And you, Bethlehem Ephrata, are a little one among the thousands of Judah. From you will go forth he who shall be the ruler in Israel, and his landing place has been set from the beginning, from the days of eternity.
“Amma ke, Betlehem ta Efrata, ko da yake ke ƙarama ce daga cikin zuriyarki a Yahuda, daga cikinki wani zai zo domina wanda zai yi mulkin Isra’ila, wanda asalinsa tun fil azal ne.”
3 Because of this, he will provide for them, even until the time in which she who bears him gives birth. And the remnant of his brothers will be converted to the sons of Israel.
Saboda haka za a yashe Isra’ila har sai wadda take naƙuda ta haihu sauran’yan’uwansa kuma sun dawo su haɗu da Isra’ilawa.
4 And he will stand firm and feed on the strength of the Lord, according to the sublime name of the Lord his God. And they will be converted, for now he will be magnified, even to the ends of the earth.
Zai tsaya yă yi kiwon garkensa da ƙarfin Ubangiji, cikin girman sunan Ubangiji Allahnsa. Za su kuma zauna lafiya, gama girmansa za tă kai har ƙarshen duniya.
5 And this man will be our peace, when the Assyrian will come into our land, and when he will trample on our houses; and we will raise against him seven shepherds and eight principal men.
Zai kuma zama salamarsu. Sa’ad da Assuriyawa suka kawo wa ƙasarmu hari suka tattake kagarunmu, za mu tā da makiyaya bakwai, har ma shugabannin mutane takwas su yi gāba da su.
6 And they will graze on the land of Assur with the sword, and the land of Nimrod with its spears; and he will free us from Assur, when he will come into our land, and when he will trample our borders.
Za su yi mulkin ƙasar Assuriya da takobi, ƙasar Nimrod kuma da zaran takobi. Zai cece mu daga hannun Assuriyawa sa’ad da suka kawo wa ƙasarmu hari suka kuma tattake zuwa cikin iyakokinmu.
7 And there will be a remnant of Jacob in the midst of many peoples, like a dew from the Lord and like drops upon the grass, which awaits no man and does not stand before the sons of men.
Raguwar Yaƙub za tă kasance a tsakiyar mutane masu yawa kamar raɓa daga Ubangiji, kamar yayyafi a kan ciyawa, wanda ba ya jiran mutum ko kuma yă dakata wa ɗan adam.
8 And there will be a remnant of Jacob within the Gentiles, in the midst of many peoples, like a lion among the beasts of the forests, and like a young lion among the flocks of sheep, who, when he will pass through and trample down and seize, there is none who can rescue.
Raguwar Yaƙub za tă kasance tare da al’ummai, a cikin mutane masu yawa, kamar zaki a cikin sauran namun jeji, kamar ɗan zaki cikin garken tumaki, wanda yake tattaka yă kuma yi kaca-kaca da su sa’ad da yake ratsa a cikinsu, ba kuwa wanda zai cece su.
9 Your hand will be exalted over your enemies, and all your adversaries will pass away.
Za a ɗaga hannunka cikin nasara a kan abokan gābanka, za a hallaka maƙiyanka duka.
10 And it will be in that day, says the Lord: I will take away your horses from your midst, and I will utterly ruin your four-horse chariots.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji “Zan hallaka dawakanku daga cikinku, in kuma rurrushe kekunan yaƙinku.
11 And I will destroy the cities of your land, and I will pull down all your fortifications,
Zan hallaka biranen ƙasarku in yi rugu-rugu da dukan katangunku.
12 and I will take away evil-doing from your hand, and there will be no divinations among you.
Zan kawar da maitarku, ba za a ƙara yin sihiri ba.
13 And I will cause your graven images to perish, and your statues, from your midst. And you will no longer adore the works of your hands.
Zan sassare dukan gumakan da kuka sassaƙa da keɓaɓɓun duwatsunku a cikinku, nan gaba ba za ku ƙara rusuna wa aikin hannuwanku ba.
14 And I will root out your sacred groves from your midst, and I will crush your cities.
Zan tumɓuke daga gare ku ginshiƙan Asheranku in kuma rurrushe biranenku.
15 And I will exact vengeance, in fury and in indignation, among all the nations which have not listened.
Zan yi ramuwa cikin fushi da hasala a kan al’umman da ba su yi mini biyayya ba.”

< Micah 5 >