< Micah 2 >

1 Woe to you who devise useless things and who work evil in your beds. In the morning light, they undertake it, because their hand is against God.
Taku ta ƙare, ku da kuke shirya makirci, ku da kuke ƙulle-ƙullen mugunta a kan gadonku! Da gari ya waye sai ku fita ku aikata mugunta domin ikon aikatawa yana hannunku.
2 And they have desired fields and have taken them by violence, and they have stolen houses. And they have made false accusations against a man and his house, a man and his inheritance.
Kukan yi ƙyashin gonaki ku kuma ƙwace su, ku yi ƙyashin gidaje ku kuma ƙwace. Kukan zalunci mutum, ku ƙwace masa gidansa, har ku ƙwace masa gādonsa.
3 For this reason, thus says the Lord: Behold, I devise an evil against this family, from which you will not steal away your necks. And you will not walk in arrogance, because this is a most wicked time.
Saboda haka, Ubangiji ya ce, “Ina shirya wa waɗannan mutane bala’i, yadda ba za ku iya ceton kanku ba. Ba za ku ƙara tafiya kuna taƙama ba, gama zai zama lokacin bala’i ne.
4 In that day, a parable will be taken up about you, and a song will be sung with sweetness, saying: “We have been devastated by depopulation.” The fate of my people has been altered. How can he withdraw from me, when he might be turned back, he who might tear apart our country?
A wannan rana mutane za su yi muku ba’a za su yi muku gwalo da wannan waƙar makoki, ‘An lalatar da mu sarai; an rarraba mallakar mutanena. Ya ɗauke shi daga gare ni! Ya miƙa filayenmu ga maciyan amanarmu.’”
5 Because of this, there will be for you no casting of the cord of fate in the assembly of the Lord.
Saboda haka ba za ku kasance da wani a taron jama’ar Ubangiji da zai raba ƙasar ta wurin jefa ƙuri’a ba.
6 Do not speak by saying, “It will not drop on these ones; shame will not embrace them.”
“Kada ku yi annabci” in ji annabawansu. “Kada ku yi annabci game da waɗannan abubuwa; abin kunya ba zai same mu ba.”
7 The house of Jacob says, “Has the Spirit of the Lord been weakened, or are such things his thoughts?” Are not my words good for him who walks uprightly?
Daidai ne a ce, ya gidan Yaƙub, “Ruhun Ubangiji yana fushi ne? Yana yin irin waɗannan abubuwa?” “Ashe, maganata ba tă amfane wanda ayyukansa suke daidai ba?
8 But, to the contrary, my people have risen up in opposition. You have lifted the cover from the undergarment, and those who passed by harmlessly, you have converted into war.
Ba da daɗewa ba mutanena sun tashi kamar magabci. Kun tuɓe riga mai tsada daga waɗanda suke wucewa ba tare da kun damu ba, sai ka ce mutanen da suke komowa daga yaƙi.
9 You have evicted the women among my people from their delicate houses. You have taken my praise forever from their little ones.
Kun kori matan mutanena daga gidajensu masu daɗi. Kuka kawar da albarkata har abada daga wurin’ya’yansu.
10 Rise and depart, for there is no relief for you here. Because of its uncleanness, it will be corrupted with a most wicked decay.
Ku tafi, ku ba ni wuri! Gama wannan ba wurin hutunku ba ne, gama ya ƙazantu, ya zama kangon da ya wuce gyara.
11 I wish that I were not a man who has breath, and that I rather spoke a lie. I will drop it down to you in wine and in drunkenness. And it will be this people on whom it will rain down.
In maƙaryaci da mazambaci ya zo ya ce, ‘Zan yi muku annabci ku sami wadataccen ruwan inabi da barasa,’ zai dai zama annabin da ya dace da wannan mutane ne!
12 I will gather together in a congregation all of you, Jacob. I will lead together as one, the remnant of Israel. I will set them together like a flock in the fold, like a sheep in the midst of the sheep pen. They will cause a tumult before the multitude of men.
“Tabbatacce zan tattara ku duka, ya gidan Yaƙub; zan tattara ku raguwar Isra’ila. Zan kawo su wuri ɗaya kamar tumaki a cikin garke, kamar garke a wajen kiwonsa; wurin zai cika da mutane.
13 For he will ascend, opening the way before them. They will separate, and they will cross the gate and enter through it. And their king will pass by, before their very eyes, and the Lord will be at their head.
Wanda ya fasa ƙofa ya buɗe, shi zai haura yă yi musu jagora, za su fashe bangon su fita. Sarkinsu zai wuce gabansu, Ubangiji kuma zai kasance a gaba.”

< Micah 2 >