< Malachi 2 >

1 And now, O priests, this command is to you.
“Yanzu fa wannan gargaɗi dominku ne, ku firistoci.
2 If you will refuse to listen, and if you will refuse to take it to heart, so as to give glory to my name, says the Lord of hosts, I will send destitution upon you, and I will curse your blessings; yes, I will curse them. For you have not taken it to heart.
In ba ku saurara ba, in kuma ba ku sa zuciyarku ga girmama sunana ba, zan aukar muku da la’ana, zan kuma la’antar da albarkunku. I, na riga na la’anta su, domin ba ku sa zuciyarku ga girmama ni ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
3 Behold, I will cast forth an arm to you, and I will scatter across your face the dung of your solemnities, and it will take you to itself.
“Saboda ku zan tsawata wa zuriyarku; zan watsa kashin dabbobin hadayunku a fuskokinku, a kuma kwashe ku tare da shi.
4 And you will know that I sent you this commandment, so that my covenant might be with Levi, says the Lord of hosts.
Za ku kuwa san cewa ni ne na aika muku da wannan gargaɗi domin alkawarina da Lawi yă ci gaba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
5 My covenant was with him for life and peace. And I gave him fear, and he feared me, and he was afraid before the face of my name.
“Alkawarina da shi, alkawari ne na rai da salama, wanda na ba shi; domin yă girmama ni, ya kuwa girmama ni, ya kuma ji tsoron sunana ƙwarai.
6 The law of truth was in his mouth, and iniquity was not found on his lips. He walked with me in peace and integrity, and he turned away many from iniquity.
Umarnin gaskiya yana a bakinsa, ba a kuma sami wani ƙarya a leɓunansa ba. Ya yi tafiya tare da ni cikin salama da adalci, ya kuwa juyo da mutane masu yawa daga zunubi.
7 For the lips of the priests will keep knowledge, and they will request the law from his mouth, because he is an angel of the Lord of hosts.
“Gama ya kamata leɓunan firist su kiyaye ilimi, ya kamata kuma mutane su nemi umarni daga bakinsa, domin shi ne manzon Ubangiji Maɗaukaki.
8 But you have withdrawn from the way, and you have scandalized very many in the law. You have nullified the covenant of Levi, says the Lord of hosts.
Amma sai kuka kauce hanya, ta wurin koyarwarku kuma kuka sa mutane da yawa suka yi tuntuɓe; kun keta alkawarin da na yi da Lawi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 Because of this, I also have made you contemptible and debased to all the people, just as you have not served my ways, and you have accepted a face in the law.
“Saboda haka na sa a rena ku, a kuma wulaƙanta ku a gaban dukan mutane, domin ba ku bi hanyoyina ba amma kuka nuna sonkai a al’amuran shari’a.”
10 Is there not one Father of us all? Did not one God create us? Why, then, does each one of us despise his brother, violating the covenant of our fathers?
Ashe, ba Mahaifi guda dukanmu muke da shi ba? Ba Allah ɗaya ne ya halicce mu ba? Don me muka keta alkawarin kakanninmu ta wurin cin amanar juna?
11 Judah has transgressed, and abomination has been committed in Israel and in Jerusalem. For Judah has contaminated the sanctified of the Lord, which he loved, and has held the daughter of a strange god.
Yahuda ya ci amana. An yi abin kunya a Isra’ila da kuma a Urushalima. Yahuda ya ƙazantar da wuri mai tsarkin da Ubangiji yake ƙauna, ta wurin auren’yar wani baƙon allah.
12 The Lord will drive away the man who has done this, both the teacher and the disciple, from the tabernacles of Jacob and from those offering a gift to the Lord of hosts.
Game da mutumin da ya aikata wannan, ko wane ne shi, bari Ubangiji yă yanke shi daga tentunan Yaƙub, ko da ma ya kawo hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki.
13 And you have done this repeatedly: you have covered the altar of the Lord with tears, with weeping and bellowing, to such an extent that I no longer have respect towards the sacrifice, nor do I accept any appeasement that is from your hands.
Ga kuma wani abin da kuke yi. Kukan cika bagaden Ubangiji da hawaye. Kukan yi kuka kuna ihu gama Ubangiji ba ya mai da hankali ga hadayunku ko yă karɓe su da farin ciki.
14 And you have said, “What is the reason for this?” It is because the Lord has been a witness between you and the wife of your youth, whom you have despised. Yet she was your partner, and the wife of your covenant.
Kukan ce, “Don me ba ya karɓan hadayunmu?” Ai, domin Ubangiji ya zama shaida tsakaninka da matar ƙuruciyarka, gama ka keta amanar da ka yi mata, ko da yake ita abokiyar zamanka ce, matar aurenka ta alkawari.
15 Did not One make her, and is she not the remainder of his spirit? And what does one seek, except offspring of God? So then, preserve your spirit, and do not despise the wife of your youth.
Ashe, Ubangiji bai maishe su ɗaya ba? Cikin jiki da ruhu, su nasa ne. Me ya sa suke ɗaya? Domin yana neman’ya’ya masu tsoron Allah. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amanar matar ƙuruciyarka.
16 If you would hold hatred, dismiss her, says the Lord, the God of Israel. But iniquity will cover his garment, says the Lord of hosts. Preserve your spirit, and do not be willing to despise.
“Na ƙi kisan aure,” in ji Ubangiji, Allah na Isra’ila. “Na kuma ƙi mutumin da ya rufe kansa da tashin hankali kamar riga,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amana.
17 You have wearied the Lord with your speeches, and you have said, “In what way, have we wearied him?” In that you say, “Everyone who does evil is good in the sight of the Lord, and such as these please him,” or certainly, “Where is the God of judgment?”
Kun sa Ubangiji Maɗaukaki ya gaji da maganganunku. Sai kuka ce, “Yaya muka sa ya gaji?” Kun yi haka ta wurin cewa, “Duk waɗanda suke aikata mugunta, mutanen kirki ne a gaban Ubangiji, yana kuwa jin daɗinsu,” kuna kuma cewa, “Ina Allah mai adalci yake?”

< Malachi 2 >