< Malachi 1 >

1 The burden of the word of the Lord to Israel by the hand of Malachi.
Annabci, wannan ita ce maganar Ubangiji ga Isra’ila ta wurin Malaki.
2 I have loved you, says the Lord, and you have said, “In what way have you loved us?” Was not Esau brother to Jacob, says the Lord? And have I not loved Jacob,
“Na ƙaunace ku, in ji Ubangiji. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya ka ƙaunace mu?’ “Isuwa ba ɗan’uwan Yaƙub ba ne?” In ji Ubangiji. “Duk da haka na ƙaunaci Yaƙub,
3 but held hatred for Esau? And I have set his mountains in solitude, and his inheritance with the serpents of the desert.
amma na ƙi Isuwa, na kuma mai da ƙasarsa da take kan duwatsu kango, na ba da gādonsa ga dilolin hamada.”
4 But if Idumea will say, “We have been destroyed, but when we return, we will build up what has been destroyed,” thus says the Lord of hosts: They will build up, and I will destroy. And they will be called “The limits of impiety,” and, “The people with whom the Lord has been angry, even to eternity.”
Edom zai iya cewa, “Ko da yake an ragargaza mu, ai, za mu sāke gina kufanmu.” Amma ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Za su iya gini, amma zan rushe. Za a ce da su Muguwar Ƙasa, mutane da kullum suke a ƙarƙashi fushin Ubangiji.
5 And your eyes will see. And you will say, “May the Lord be magnified beyond the limits of Israel.”
Za ku ga wannan da idanunku ku kuma ce, ‘Ubangiji da girma yake, har gaba da iyakokin Isra’ila ma!’
6 The son honors the father, and the servant his master. If, therefore, I am Father, where is my honor? And if I am Master, where is my fear? says the Lord of hosts to you, O priests, who despise my name. And you have said, “In what way, have we despised your name?”
“Ɗa yakan girmama mahaifinsa, bawa kuma yakan girmama maigidansa. In ni mahaifi ne, ina girman da ya dace da ni? In ni maigida ne, ina girman da ya dace da ni?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Ku firistoci, ku ne kuka rena sunana. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka rena sunanka?’
7 You offer polluted bread upon my altar, and you say, “In what way, have we polluted you?” In that you say, “The table of the Lord has been despised.”
“Kun ajiye abinci mai ƙazanta a kan bagadena. “Sai kuka ce, ‘Yaya muka ƙazantar da kai?’ “Ta wurin cewa teburin Ubangiji abin reni ne.
8 If you offer the blind for sacrifice, is this not evil? And if you offer the lame and the sick, is this not evil? Offer it to your leader, if he will be pleased with it, or if he will accept your face, says the Lord of hosts.
Sa’ad da kuka kawo makauniyar dabba don ku miƙa mini hadaya, wannan daidai ne? Sa’ad da kuka miƙa gurguwar dabba ko marar lafiya, wannan daidai ne? Ku gwada ba wa gwamnanku irin wannan ku gani! Kuna gani zai ji daɗinku? Zai karɓe ku ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 And now, beseech the face of God, so that he may have mercy on you (for by your hand has this been done) if, in any way, he might accept your faces, says the Lord of hosts.
“To, firistoci yanzu ku gwada ku roƙi Allah yă yi mana alheri. Da irin hadayun nan a hannuwanku ne zai ji ku?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
10 Who is there among you that would close the doors and enflame my altar without pay? I have no favor in you, says the Lord of hosts. And I will not accept a gift from your hand.
“Kash, da ma wani daga cikinku ya rufe ƙofofin haikali don kada ku shiga, ku hura wuta marar amfani a bisa bagadena! Ba na jin daɗinku, ba zan kuwa karɓi hadaya daga hannuwanku ba” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
11 For, from the rising of the sun even to its setting, my name is great among the Gentiles, and in every place, a clean oblation is being sacrificed and offered to my name. For my name is great among the Gentiles, says the Lord of hosts.
Sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta. A kowane wuri za a miƙa wa sunana turare da tsabtacciyar hadaya domin sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
12 And you have polluted it, in that you say, “The table of the Lord has been contaminated; and that which is placed upon it is contemptible, compared with the fire that devours it.”
“Amma kun ƙazantar da sunana ta wurin cewa ‘Teburin Ubangiji ya ƙazantu,’ kuka kuma yi magana a kan abincinsa kuna cewa, ‘Abin reni ne.’
13 And you have said, “Behold our labor,” and you have exhaled it away, says the Lord of hosts. And you brought in by plunder the lame, and the sick, and brought it in as a gift. How can I receive this from your hand, says the Lord?
Kun kuma ce, ‘Mun gaji da irin wannan wahala!’ Kuna hura mini hancin reni,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Sa’ad da kuka kawo raunannu, gurguntattun dabbobi, ko kuma dabbobi masu fama da cuta, kuka kuma miƙa su hadaya, kuna gani zan karɓi wannan daga gare ku?” In ji Ubangiji.
14 Cursed is the deceitful, who holds in his flock a male, and, when making a vow, offers in sacrifice that which is feeble to the Lord. For I am a great King, says the Lord of hosts, and my name is dreadful among the Gentiles.
“La’ananne ne macucin da yake da lafiyayyiyar dabba namiji a garkensa wadda ya yi alkawari zai bayar, amma sai ya miƙa hadayar dabba mai aibi ga Ubangiji. Gama ni babban sarki ne, za a kuma ji tsoron sunana a cikin al’ummai,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.

< Malachi 1 >