< Luke 1 >

1 Since, indeed, many have attempted to set in order a narrative of the things that have been completed among us,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 just as they have been handed on to those of us who from the beginning saw the same and were ministers of the word,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 so it seemed good to me also, having diligently followed everything from the beginning, to write to you, in an orderly manner, most excellent Theophilus,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 so that you might know the truthfulness of those words by which you have been instructed.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 There was, in the days of Herod, king of Judea, a certain priest named Zechariah, of the section of Abijah, and his wife was of the daughters of Aaron, and her name was Elizabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Now they were both just before God, progressing in all of the commandments and the justifications of the Lord without blame.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 And they had no child, because Elizabeth was barren, and they both had become advanced in years.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Then it happened that, when he was exercising the priesthood before God, in the order of his section,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 according to the custom of the priesthood, the lot fell so that he would offer incense, entering into the temple of the Lord.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 And the entire multitude of the people was praying outside, at the hour of incense.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Then there appeared to him an Angel of the Lord, standing at the right of the altar of incense.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 And upon seeing him, Zechariah was disturbed, and fear fell over him.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 But the Angel said to him: “Do not be afraid, Zechariah, for your prayer has been heard, and your wife Elizabeth shall bear a son to you. And you shall call his name John.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 And there will be joy and exultation for you, and many will rejoice in his nativity.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 For he will be great in the sight of the Lord, and he will not drink wine or strong drink, and he will be filled with the Holy Spirit, even from his mother’s womb.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 And he will convert many of the sons of Israel to the Lord their God.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 And he will go before him with the spirit and power of Elijah, so that he may turn the hearts of the fathers to the sons, and the incredulous to the prudence of the just, so as to prepare for the Lord a completed people.”
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 And Zechariah said to the Angel: “How may I know this? For I am elderly, and my wife is advanced in years.”
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 And in response, the Angel said to him: “I am Gabriel, who stands before God, and I have been sent to speak to you, and to proclaim these things to you.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 And behold, you will be silent and unable to speak, until the day on which these things shall be, because you have not believed my words, which will be fulfilled in their time.”
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 And the people were waiting for Zechariah. And they wondered why he was being delayed in the temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Then, when he came out, he was unable to speak to them. And they realized that he had seen a vision in the temple. And he was making signs to them, but he remained mute.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 And it happened that, after the days of his office were completed, he went away to his house.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Then, after those days, his wife Elizabeth conceived, and she hid herself for five months, saying:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 “For the Lord did this for me, at the time when he decided to take away my reproach among men.”
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Then, in the sixth month, the Angel Gabriel was sent by God, to a city of Galilee named Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 to a virgin betrothed to a man whose name was Joseph, of the house of David; and the name of the virgin was Mary.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 And upon entering, the Angel said to her: “Hail, full of grace. The Lord is with you. Blessed are you among women.”
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 And when she had heard this, she was disturbed by his words, and she considered what kind of greeting this might be.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 And the Angel said to her: “Do not be afraid, Mary, for you have found grace with God.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Behold, you shall conceive in your womb, and you shall bear a son, and you shall call his name: JESUS.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 He will be great, and he will be called the Son of the Most High, and the Lord God will give him the throne of David his father.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 And he will reign in the house of Jacob for eternity. And his kingdom shall have no end.” (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Then Mary said to the Angel, “How shall this be done, since I do not know man?”
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 And in response, the Angel said to her: “The Holy Spirit will pass over you, and the power of the Most High will overshadow you. And because of this also, the Holy One who will be born of you shall be called the Son of God.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 And behold, your cousin Elizabeth has herself also conceived a son, in her old age. And this is the sixth month for her who is called barren.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 For no word will be impossible with God.”
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Then Mary said: “Behold, I am the handmaid of the Lord. Let it be done to me according to your word.” And the Angel departed from her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 And in those days, Mary, rising up, traveled quickly into the hill country, to a city of Judah.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 And she entered into the house of Zechariah, and she greeted Elizabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 And it happened that, as Elizabeth heard the greeting of Mary, the infant leaped in her womb, and Elizabeth was filled with the Holy Spirit.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 And she cried out with a loud voice and said: “Blessed are you among women, and blessed is the fruit of your womb.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 And how does this concern me, so that the mother of my Lord would come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For behold, as the voice of your greeting came to my ears, the infant in my womb leaped for joy.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 And blessed are you who believed, for the things that were spoken to you by the Lord shall be accomplished.”
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 And Mary said: “My soul magnifies the Lord.
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 And my spirit leaps for joy in God my Savior.
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 For he has looked with favor on the humility of his handmaid. For behold, from this time, all generations shall call me blessed.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 For he who is great has done great things for me, and holy is his name.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 And his mercy is from generation to generations for those who fear him.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He has accomplished powerful deeds with his arm. He has scattered the arrogant in the intentions of their heart.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He has deposed the powerful from their seat, and he has exalted the humble.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 He has filled the hungry with good things, and the rich he has sent away empty.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 He has taken up his servant Israel, mindful of his mercy,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 just as he spoke to our fathers: to Abraham and to his offspring forever.” (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Then Mary stayed with her for about three months. And she returned to her own house.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Now the time for Elizabeth to give birth arrived, and she brought forth a son.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 And her neighbors and relatives heard that the Lord had magnified his mercy with her, and so they congratulated her.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 And it happened that, on the eighth day, they arrived to circumcise the boy, and they called him by his father’s name, Zechariah.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 And in response, his mother said: “Not so. Instead, he shall be called John.”
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 And they said to her, “But there is no one among your relatives who is called by that name.”
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Then they made signs to his father, as to what he wanted him to be called.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 And requesting a writing tablet, he wrote, saying: “His name is John.” And they all wondered.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Then, at once, his mouth was opened, and his tongue loosened, and he spoke, blessing God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 And fear fell upon all of their neighbors. And all these words were made known throughout all the hill country of Judea.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 And all those who heard it stored it up in their heart, saying: “What do you think this boy will be?” And indeed, the hand of the Lord was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 And his father Zechariah was filled with the Holy Spirit. And he prophesied, saying:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 “Blessed is the Lord God of Israel. For he has visited and has wrought the redemption of his people.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 And he has raised up a horn of salvation for us, in the house of David his servant,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 just as he spoke by the mouth of his holy Prophets, who are from ages past: (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 salvation from our enemies, and from the hand of all those who hate us,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 to accomplish mercy with our fathers, and to call to mind his holy testament,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 the oath, which he swore to Abraham, our father, that he would grant to us,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 so that, having been freed from the hand of our enemies, we may serve him without fear,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 in holiness and in justice before him, throughout all our days.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And you, child, shall be called the prophet of the Most High. For you will go before the face of the Lord: to prepare his ways,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 to give knowledge of salvation to his people for the remission of their sins,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 through the heart of the mercy of our God, by which, descending from on high, he has visited us,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 to illuminate those who sit in darkness and in the shadow of death, and to direct our feet in the way of peace.”
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And the child grew, and he was strengthened in spirit. And he was in the wilderness, until the day of his manifestation to Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >