< Leviticus 8 >

1 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Take Aaron, with his sons, their vestments, and the oil of anointing, a calf for sin, two rams, and a basket with unleavened bread,
“Kawo Haruna da’ya’yansa maza, ka ɗauki rigunansu, man keɓewa, bijimi domin hadaya don zunubi,’yan raguna biyu da kuma kwandon da yake da burodi marar yisti,
3 and gather together all the assembly at the door of the tabernacle.
ka kuma tara dukan jama’a a ƙofar Tentin Sujada.”
4 And Moses did as the Lord had commanded. And when all the crowd was gathered together before the entrance of the tabernacle,
Sai Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi, jama’a kuwa suka taru a ƙofar Tentin Sujada.
5 he said: “This is the word that the Lord has ordered to be done.”
Sai Musa ya ce wa jama’ar, “Ga abin da Ubangiji ya umarta a yi.”
6 And immediately, he brought forward Aaron and his sons. And when he had washed them,
Sa’an nan Musa ya kawo Haruna da’ya’yansa maza gaba, ya kuma wanke su da ruwa.
7 he vested the high priest with the linen undergarment, wrapped him with the wide belt, and clothed him with the hyacinth tunic, and over it he imposed the ephod.
Ya sa wa Haruna taguwa, ya ɗaura igiya kewaye da shi, ya sa masa riga, ya sa masa efod. Ya kuma ɗaura masa efod wanda aka yi masa saƙar gwaninta.
8 And tying it to the belt, he fitted it to the breastplate, on which was Doctrine and Truth.
Ya sa masa ƙyallen maƙalawa a ƙirji, ya kuma sa Urim da Tummim a ƙyallen maƙalawa a ƙirjin.
9 Also, he wrapped the headdress on his head, and over it, opposite the forehead, he placed the plate of gold, consecrated with sanctification, just as the Lord had instructed him.
Sai ya naɗa masa rawani, daga gaban rawanin ya sa allon zinariya, wato, kambi tsattsarka, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.
10 He also took up the oil of anointing, with which he anointed the tabernacle, along with all of its articles.
Sa’an nan Musa ya ɗauki man keɓewa ya keɓe tabanakul da kuma kowane abin da yake cikinsa, ta haka ya tsarkake su.
11 And when he had sprinkled the altar seven times to sanctify it, he anointed it and all its vessels. And the washtub with its base he sanctified with the oil.
Ya yayyafa mai a kan bagade sau bakwai, yana keɓe bagade da dukan kayayyaki, da daro, da abin da yake tsaya a kai, don yă tsarkake su.
12 And pouring the oil over Aaron’s head, he anointed and consecrated him.
Ya zuba man keɓewa a kan Haruna, ya kuma keɓe shi don yă tsarkake shi.
13 Likewise, after he had offered his sons, he vested them with linen tunics, and wrapped them with wide belts, and placed headdresses on them, just as the Lord had ordered.
Sa’an nan ya kawo’ya’yan Haruna maza, ya sa musu taguwoyi, ya ɗaɗɗaura igiyoyi kewaye da su, ya kuma sa musu huluna yadda Ubangiji ya umarce shi.
14 He also offered the calf for sin. And when Aaron and his sons had placed their hands upon its head,
Sa’an nan ya miƙa bijimi domin hadaya don zunubi, sai Haruna da’ya’yansa suka ɗibiya hannuwansu a bijimin.
15 he immolated it. And drawing the blood, and dipping his finger in it, he touched the horns of the altar all around. And when it was expiated and sanctified, he poured out the remainder of the blood at its base.
Musa ya yanka bijimin ya ɗauki jinin, ya sa yatsarsa ya zuba a dukan ƙahonin bagade don yă tsarkake bagaden. Ya zuba sauran jinin a gindin bagade. Ta haka ya tsarkake shi don yă yi kafara dominsa.
16 Yet truly, the fat which was on the vital organs, and the mesh of the liver, and the two little kidneys with their fat, he burned upon the altar.
Musa ya ɗebo dukan kitsen da yake kewaye da kayan ciki, da kuma wanda ya rufe hanta, da ƙodojin, da kuma kitsensu, ya kuma ƙone su a kan bagade.
17 And the calf with the skin, and the flesh, and the dung, he burned beyond the camp, just as the Lord had instructed.
Amma bijimin da fatarsa da namansa da kuma ƙashinsa ya ƙone su a bayan sansani, yadda Ubangiji ya umarce shi.
18 He also offered a ram as a holocaust. And when Aaron and his sons had imposed their hands upon its head,
Sa’an nan ya miƙa ɗan rago domin hadaya ta ƙonawa, sai Haruna da’ya’yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan ɗan rago.
19 he immolated it, and he poured out its blood around the altar.
Sa’an nan Musa ya yanka ɗan ragon, ya kuma yayyafa jinin a kowane gefe na bagaden.
20 And cutting the ram into pieces, he burned its head, and the limbs, and the fat in the fire,
Ya yanka ragon gunduwa-gunduwa ya ƙone kan, ya kuma ƙone gunduwa-gunduwan da kitsen.
21 having first washed the intestines and the feet. And then he burned the whole of the ram upon the altar, because it was a holocaust of most sweet odor to the Lord, just as he had instructed him.
Ya wanke kayan cikin da ƙafafun a ruwa, ya kuma ƙone dukan ragon a bisa bagade kamar hadaya ta ƙonawa, mai daɗin ƙanshi, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
22 He also offered the second ram, as a consecration of priests. And Aaron and his sons placed their hands upon its head.
Sai ya miƙa ɗayan ɗan ragon, ɗan ragon naɗin, sai Haruna da’ya’yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan ɗan ragon.
23 And when Moses had immolated it, taking up some of its blood, he touched the tip of Aaron’s right ear, and the thumb of his right hand, and similarly also his foot.
Musa kuwa ya yanka ɗan ragon ya ɗibi jinin ya sa leɓatun kunnen dama na Haruna, ya kuma sa a babbar yatsarsa ta hannun dama da kuma a babbar yatsar ƙafarsa ta dama.
24 He also offered the sons of Aaron. And when, from the blood of the ram which was immolated, he had touched the tip of the right ear of each one, and the thumbs of their right hands, as well as their feet, he poured out the remainder upon the altar all around.
Musa ya kuma kawo’ya’yan Haruna gaba, ya sa jini a leɓatun kunnuwansu na dama, ya kuma sa a manyan yatsotsinsu na hannun dama da kuma a manyan yatsotsinsu na ƙafafunsu na dama. Sa’an nan ya yayyafa jinin a kowane gefen bagade.
25 Yet truly, the fat, and the rump, and all the fat that covers the intestines, and the mesh of the liver, and the two kidneys with their fat, and the right shoulder, he separated.
Ya ɗibi kitsen, da wutsiya mai kitse, da kuma dukan kitsen da ke kewaye da kayan ciki, da wanda ya rufe hanta, ƙodoji biyu da kitsensu da kuma cinya ta dama.
26 Then, taking bread without leaven from the basket of unleavened bread, which was before the Lord, and a cake sprinkled with oil, and a wafer, he placed them upon the fat and the right shoulder,
Sa’an nan daga cikin kwandon burodi marar yisti wanda yake a gaban Ubangiji, ya ɗauko dunƙulen burodi, da kuma guda da aka yi da mai, da kuma ƙosai; ya sa waɗannan a sassan kitsen, da kuma a cinya ta dama.
27 delivering all these to Aaron and his sons. And when they had lifted them up in the sight of the Lord,
Ya sa waɗannan a hannuwan Haruna da’ya’yansa, suka kuma kaɗa su a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa.
28 he received them again from their hands, and he burned them upon the altar of holocaust, because it was an oblation of consecration, as a sweet odor of sacrifice to the Lord.
Sa’an nan Musa ya karɓe su daga hannuwansu ya ƙone a bagade a bisa hadaya ta ƙonawa a matsayin hadaya ta naɗi, mai daɗin ƙanshi, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
29 And he took his portion from the ram of consecration, and he lifted up its breast in the sight of the Lord, just as the Lord had instructed him.
Ya kuma ɗauki ƙirjin; rabon Musa na ɗan ragon naɗi, ya kaɗa shi a gaban Ubangiji, a matsayin hadaya ta kaɗawa, yadda Ubangiji ya umarce shi.
30 And taking up the ointment, and the blood that was on the altar, he sprinkled it over Aaron and his vestments, and over his sons and their vestments.
Sai Musa ya ɗibi man keɓewa da jini daga bagade, ya yayyafa su a kan Haruna da rigunansa, da kuma a kan’ya’yansa da rigunansu, don yă tsarkake Haruna da rigunansa da kuma’ya’yansa da rigunansu.
31 And when he had sanctified them with their vestments, he instructed them, saying: “Cook the flesh before the entrance of the tabernacle, and eat it there. Likewise, eat the loaves of consecration, which have been placed in the basket, just as the Lord instructed me, saying: ‘Aaron and his sons shall eat them.’
Sai Musa ya ce wa Haruna da’ya’yansa maza, “Ku dafa naman a ƙofar Tentin Sujada, ku kuma ci shi a can tare da burodi daga kwandon naɗi, yadda na umarta, cewa, ‘Haruna da’ya’yansa maza za su ci shi.’
32 Then whatever will remain of the flesh and the loaves shall be consumed with fire.
Sa’an nan ku ƙone sauran naman da kuma burodin.
33 Also, you shall not exit from the door of the tabernacle for seven days, until the day on which the time of your consecration shall be completed. For in seven days the consecration is finished,
Kada ku bar ƙofar Tentin Sujada har kwana bakwai, sai ranakun naɗi suka cika, gama naɗinku zai ɗauki kwana bakwai.
34 even as it has begun at this present time, so that the rite of the sacrifice might be accomplished.
Abin da aka yi a yau umarni ne daga Ubangiji don yin kafara saboda ku.
35 Day and night you shall remain in the tabernacle, observing the watches of the Lord, otherwise you shall die. For so it has been commanded to me.”
Dole ku kasance a ƙofar Tentin Sujada dare da rana har kwana bakwai, ku kuma yi abin da Ubangiji yake bukata, don kada ku mutu; gama abin da aka umarce ni ke nan.”
36 And Aaron and his sons did everything that the Lord spoke by the hand of Moses.
Saboda haka Haruna da’ya’yansa maza suka yi kome da Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.

< Leviticus 8 >