< Leviticus 7 >

1 Likewise, this is the law of the sacrifice for a transgression. It is the Holy of holies.
“‘Waɗannan su ne ƙa’idodi na hadaya don laifi, hadaya ce tsattsarka.
2 Therefore, where the holocaust is immolated, the victim for a transgression shall also be slain. Its blood shall be poured out all around the altar.
Za a yanka hadaya don laifi a inda ake yanka hadaya ta ƙonawa, za a kuma yayyafa jinin a kowane gefe na bagade.
3 They shall offer from it: the rump, and the fat that covers the vital organs,
Za a miƙa kitsen abin hadaya duka, da wutsiya mai kitse, da kitsen da yake rufe da kayan ciki,
4 the two little kidneys, and the fat that is near the sides, and the mesh of the liver with the little kidneys.
da ƙodoji biyu da kitsen da yake a bisansu kusa da kwiɓi, da kuma rufin hanta, wanda za a cire tare da ƙodoji.
5 And the priest shall burn them upon the altar. It is the incense of the Lord on behalf of a transgression.
Firist zai ƙone su a kan bagade, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji. Hadaya ce don laifi.
6 Every male of priestly descent shall feed on this flesh in a holy place, because it is the Holy of holies.
Kowane da namiji cikin iyalin firistoci zai iya ci. Sai a tsattsarkan wuri ne za a ci; gama abu mafi tsarki ne.
7 Just as the sacrifice for sin is offered, so also for a transgression; one law shall be for both sacrifices. It shall belong to the priest who offers it.
“‘Hadaya don laifi kamar hadaya don zunubi take, saboda haka ƙa’ida hanyar yinsu iri ɗaya ce. Su ɗin na firist da ya yi kafara da su ne.
8 The priest who offers the victim of holocaust shall have its skin.
Firist da ya miƙa hadaya ta ƙonawa domin wani, zai iya ajiye fatar wa kansa.
9 And every sacrifice of fine wheat flour which is baked in the oven, and whatever is prepared on the oven grating or in the frying pan, shall be for the priest who offers it.
Kowace hadaya ta garin da aka toya a tanda, ko aka dafa a tukunya ko a kan kaskon tuya, na firist da ya miƙa ta ne,
10 Whether these will be sprinkled with oil, or left dry, an equal measure shall be divided to each one of the sons of Aaron.
kuma kowace hadaya ta gari wadda aka kwaɓa da mai, ko wadda ba a kwaɓa ba, ita ma, ta dukan’ya’ya Haruna ne maza.
11 This is the law of the victim of peace offerings, which is offered to the Lord.
“‘Waɗannan su ne ƙa’idodin hadaya don zumuncin da mutum zai iya miƙa ga Ubangiji.
12 If the oblation will be an act for giving thanks, they shall offer bread without leaven sprinkled with oil, and unleavened wafers anointed with oil, and fine wheat flour fried, and cakes sprinkled and mixed with oil,
“‘In ya miƙa hadayar a matsayin hadaya ta godiya ce, to, zai miƙa ta tare da burodi mai kauri marar yisti, wanda aka kwaɓa da mai, da burodi marar kauri, wanda aka shafa wa mai, da kuma burodi mai kauri da aka yi da gari mai laushi wanda aka kwaɓa sosai da mai.
13 and also, leavened bread with the sacrifice of thanksgiving, which is immolated for peace offerings.
Tare da hadayarsa don zumunci ta godiya, zai miƙa dunƙulen burodin da aka yi da yisti.
14 Of these, one shall be offered to the Lord as the first-fruits, and one shall be for the priest who will pour out the blood of the victim.
Zai kuma kawo ɗaya daga kowace a matsayin hadaya, baiko ne ga Ubangiji. Wannan zai zama na firist da ya yafa jinin hadaya ta salama ne.
15 The flesh of it shall be eaten on the same day; neither shall any of it remain until morning.
Za a ci wannan nama na hadaya don zumunci ta godiya a ranar da aka miƙa ta, kada yă bar wani abu daga naman yă kwana.
16 If anyone, by a vow or of his own accord, will have offered a sacrifice, it shall be eaten in a similar manner on the same day. But then if any of it will have remained until tomorrow, it is lawful to eat it.
“‘In hadayarsa cika wa’adin rantsuwa ce ko kuwa ta yardar rai ce, sai a ci hadayar a ranar da ya miƙa ta, amma za a iya cin duk abin da ya rage kashegari.
17 Then whatever will be found on the third day shall be consumed with fire.
Duk naman hadayar da ya rage har kwana uku, dole a ƙone shi.
18 If anyone will have eaten from the flesh of the victim of peace offerings on the third day, the oblation will be nullified; neither will it benefit the one who offered it. But instead, whatever soul will contaminate itself with such foods will be guilty of a betrayal.
Idan aka ci naman hadayarsa ta salama a rana ta uku, ba za a karɓi wanda ya ba da hadayar har ya sami albarkar hadayar ba, naman zai zama abin ƙyama, duk wanda ya ci kuwa ya yi laifi.
19 The flesh that has touched anything unclean shall not be eaten, but it shall be burnt with fire. He that is clean will feed on it.
“‘Ba za a ci naman da ya taɓa wani abu marar tsarki ba; dole a ƙone shi. Game da sauran nama, kowa da yake mai tsarki zai iya ci.
20 If a soul which is polluted will have eaten from the flesh of the sacrifice of peace offerings, which is offered to the Lord, he shall perish from his people.
Amma in wani wanda ba shi da tsarki ya ci naman hadaya ta salama ga Ubangiji, za a fid da mutumin daga cikin mutanensa.
21 And whoever will have touched the uncleanness of man, or of beast, or of anything which is able to defile, and who will have eaten from this kind of flesh, shall be cut off from his people.
Idan wani mutum ya taɓa abu marar tsarki, ko mutum ne, ko dabba ce, ko wani abu na banƙyama, ya kuma ci naman hadaya ta salama ga Ubangiji, za a fid da mutumin daga cikin mutanensa.’”
22 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
23 Say to the sons of Israel: The fat of a sheep, and of an ox, and of a goat you shall not eat.
“Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Kada ku ci wani kitsen shanu, ko na tumaki, ko kuwa na awaki.
24 The fat of a carcass that has died on its own, or of an animal that has been seized by a wild beast, you shall have for various uses.
Za a iya yin wani amfani da kitsen dabbar da ta mutu mushe, ko kitsen dabbar da namun jeji su yayyaga, amma kada a kuskura a ci.
25 If anyone will have eaten the fat which ought to be offered as a burnt sacrifice of the Lord, he shall perish from his people.
Duk wanda ya ci kitsen dabbar da aka miƙa ta wuta ga Ubangiji, za a fid da shi daga mutanensa.
26 Likewise, you shall not take as food the blood of any animals at all, whether of birds or beasts.
Kuma duk inda kuke zama, ba za ku ci jinin wani tsuntsu ko na dabba ba.
27 Every soul that will have eaten blood shall perish from his people.
Duk wanda ya ci jini, za a fid da mutumin daga mutanensa.’”
28 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
29 Speak to the sons of Israel, saying: Whoever offers a victim of peace offerings to the Lord, let him also offer at the same time a sacrifice, that is, its libations.
“Faɗa wa Isra’ilawa, ‘Duk wanda ya kawo hadaya ta salama ga Ubangiji, sai ya kawo hadayarsa ga Ubangiji daga cikin hadayu na salama.
30 He shall hold in his hands the fat of the victim, and the breast. And when he will have offered and consecrated both to the Lord, he shall deliver them to the priest,
Da hannuwansa zai kawo hadayar da za a ƙona ga Ubangiji; zai kawo kitsen tare da ƙirjin, yă kuma kaɗa ƙirjin a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa.
31 who shall burn the fat upon the altar. But the breast shall be for Aaron and his sons.
Firist zai ƙone kitsen a bisa bagade, amma ƙirjin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza.
32 Likewise also, the right shoulder of the victim of peace offerings shall fall to the priest as first-fruits.
Za ku ba da cinya ta dama ta hadaya don zumuncinku ga firist a matsayin baiko.
33 Among the sons of Aaron, whoever will have offered the blood and the fat, the same one shall also have the right shoulder for his portion.
Ɗan Haruna da ya miƙa jini da kitsen hadaya ta salama, zai ɗauki cinyar tă zama rabonsa.
34 So then, the breast that is lifted up, and the shoulder that is separated, I have taken from the sons of Israel, from their victims of peace offerings, and I have given these to Aaron the priest and to his sons, as a law in perpetuity, from all the people of Israel.
Daga hadaya ta salama ta Isra’ilawa, na ɗauki ƙirjin da aka kaɗa da kuma cinyar da aka miƙa, na ba da su ga Haruna firist da kuma’ya’yansa maza a matsayin rabonsu na kullum daga Isra’ilawa.’”
35 This is the anointing of Aaron and his sons, by the ceremonies of the Lord, in the day when Moses offered them, so that they may fulfill the priesthood,
Wannan shi ne sashen hadayar da aka ba wa Haruna da’ya’yansa maza, hadayar da aka yi ga Ubangiji da wuta, tun ranar da aka gabatar da su don su yi wa Ubangiji hidima a matsayin firist.
36 and this is what the Lord instructed to be given to them by the sons of Israel, as a perpetual observance in their generations.
A ranar da aka keɓe su, Ubangiji ya umarta cewa Isra’ilawa su ba da wannan a gare su a matsayin rabonsu na kullum, a dukan tsararraki masu zuwa.
37 This is the law of the holocaust, and of the sacrifice for sin, and for transgression, and for consecration, and for the victims of peace offerings,
Waɗannan su ne ƙa’idodi don hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, hadaya don zunubi, hadaya don laifi, hadaya ta naɗi da kuma hadaya ta salama,
38 which the Lord appointed to Moses on mount Sinai, when he commanded the sons of Israel to offer their oblations to the Lord in the desert of Sinai.
waɗanda Ubangiji ya ba wa Musa a Dutsen Sinai, a Hamadar Sinai, a ranar da ya umarci Isra’ilawa su kawo hadayunsu ga Ubangiji.

< Leviticus 7 >