< Leviticus 19 >

1 The Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Speak to the entire assembly of the sons of Israel, and you shall say to them: Be holy, for I, the Lord your God, am holy.
“Yi wa taron jama’ar Isra’ila gaba ɗaya magana, ka ce musu, ‘Ku zama masu tsarki, domin Ni, Ubangiji Allahnku, mai tsarki ne.
3 Let each one fear his father and his mother. Observe my Sabbaths. I am the Lord your God.
“‘Dole kowannenku yă girmama mahaifiyarsa da mahaifinsa, dole kuma ku kiyaye Asabbacina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
4 Do not be willing to convert to idols, neither should you make molten gods for yourselves. I am the Lord your God.
“‘Kada ku juyo ga gumaka, ko ku yi wa kanku allolin da aka yi zubi da ƙarfe. Ni ne Ubangiji Allahnku.
5 If you immolate a victim of peace offerings to the Lord, so that he may be appeased,
“‘Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, ku miƙa ta yadda za tă karɓu a madadinku.
6 you shall eat it on the same day as when it was immolated, and the next day. Then whatever will remain on the third day you shall burn with fire.
Za a ci ta a ranar da kuka miƙa ta, ko kuwa a kashegarin; duk abin da ya rage har kwana ta uku dole a ƙone shi.
7 If anyone, after two days, will have eaten from it, he shall be profane and guilty of impiety.
In aka ci ta a rana ta uku, marar tsabta ce, ba kuma za a karɓe ta ba.
8 And he shall bear his iniquity, for he has polluted what is holy to the Lord. And that soul shall perish from his people.
Duk wanda ya ci ta zai zama da laifi domin ya ƙazantar da abin da yake da tsarki ga Ubangiji, dole a raba mutumin nan da mutanensa.
9 When you will have harvested the grain fields of your land, you shall not cut it down to the surface of the land, even to the ground, nor shall you gather the remaining ears of grain.
“‘Sa’ad da kuka yi girbin amfanin gonarku, kada ku girbe har zuwa gefen gonar, ko ku yi kalan girbinku.
10 Neither shall you gather the clusters or individual grapes which fall down in your vineyard, but you shall leave them for paupers and travelers to take. I am the Lord your God.
Kada ku koma gonar inabinku kuna kala, ko ku tattara’ya’yan inabin da suka fāffāɗi. Ku bar su domin matalauta da kuma baƙi. Ni ne Ubangiji Allahnku.
11 You shall not steal. You shall not lie. Neither shall anyone deceive his neighbor.
“‘Kada ku yi sata. “‘Kada ku yi ƙarya. “‘Kada ku ruɗe juna.
12 You shall not commit perjury in my name, nor shall you pollute the name of your God. I am the Lord.
“‘Kada ku rantse bisa ƙarya da sunana, ta haka har ku ƙasƙantar da sunan Allahnku. Ni ne Ubangiji.
13 You shall not slander your neighbor, nor shall you oppress him by violence. The wages of a hired hand, you shall not delay with you until tomorrow.
“‘Kada ku zalunci maƙwabcinku, ko ku yi masa ƙwace. “‘Kada ku riƙe albashin ma’aikaci yă kwana.
14 You shall not speak evil of the deaf, nor shall you place a stumbling block before the blind, but you shall fear the Lord your God, for I am the Lord.
“‘Kada ku zagi kurma, ko ku sa abin tuntuɓe a gaban makaho, amma ku ji tsoron Allahnku. Ni ne Ubangiji.
15 You shall not do what is unjust, nor shall you judge unjustly. You shall not consider the reputation of the poor, nor shall you honor the countenance of the powerful. Judge your neighbor justly.
“‘Kada ku yi rashin adalci cikin shari’a; kada ku nuna sonkai ga matalauci, ko ku goyi bayan mai arziki, amma ku shari’anta maƙwabci cikin gaskiya.
16 You shall not be a detractor, nor a whisperer, among the people. You shall not stand against the blood of your neighbor. I am the Lord.
“‘Kada ku yi ta yawo kuna yaɗa ƙarya a cikin mutanenku. “‘Kada ku yi wani abin da zai sa ran maƙwabcinku cikin hatsari. Ni ne Ubangiji.
17 You shall not hate your brother in your heart, but reprove him openly, lest you have sin over him.
“‘Kada ka yi ƙiyayyar ɗan’uwanka a zuciya. Ka tsawata wa maƙwabcinka da gaske don kada ka sami rabo cikin laifinsa.
18 Do not seek revenge, neither should you be mindful of the injury of your fellow citizens. You shall love your friend as yourself. I am the Lord.
“‘Kada ka nemi yin ramuwa, ko ka riƙe wani cikin mutanenka a zuciya, amma ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka. Ni ne Ubangiji.
19 Observe my laws. You shall not cause your cattle to breed with other kinds of animals. You shall not sow your field with diverse seeds. You shall not be clothed with a garment which has been woven from two things.
“‘Ku kiyaye farillaina. “‘Kada ku sa dabbobin da ba iri ɗaya ba su yi barbara. “‘Kada ku yi shuki iri biyu a gonarku. “‘Kada ku sa rigar da aka saƙa da yadi iri biyu.
20 If a man will have slept in sexual intercourse with a woman, who is a servant and who is also able to be married, and yet he has not redeemed her with a price, nor paid to set her free, they both shall be beaten, but they shall not die, for she was not a free woman.
“‘In wani ya kwana da mace wadda take baiwa, wadda aka yi wa wani alkawari amma bai fanshe ta ba, ko kuwa ba a’yantar da ita ba, dole a yi hukuncin da ya dace. Duk da haka ba za a kashe su ba, domin ba a’yantar da ita ba.
21 But, for his offense, he shall offer a ram to the Lord at the door of the tabernacle of the testimony.
Dole mutumin da ya kwana da ita yă kawo rago a ƙofar Tentin Sujada domin hadaya don laifi ga Ubangiji.
22 And the priest shall pray for him, and for his sin, before the Lord, and he shall win his favor again for him, and the sin shall be forgiven.
Da ragon hadaya don laifin ne firist zai yi kafara saboda mutumin a gaban Ubangiji saboda zunubin da ya yi, za a kuwa gafarta zunubinsa.
23 When you will have entered into the land, and will have planted in it fruit trees, you shall take away their first-fruits; the fruit that germinates shall be unclean to you, neither shall you eat from these.
“‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar kuka kuma shuka kowane irin itace mai’ya’ya na ci, ku ɗauki’ya’yan itatuwan nan a matsayi an hana ku ci. Shekara uku za ku ɗauka a matsayi an hana ku, ba za ku ci su ba.
24 But in the fourth year, all their fruit shall be sanctified for the praise of the Lord.
A shekara ta huɗu, dukan’ya’yansu za su zama tsarkakakku, hadaya ta yabo ga Ubangiji.
25 And in the fifth year you shall eat the produce, gathering the fruits which are brought forth. I am the Lord your God.
Amma a shekara ta biyar, za ku iya cin’ya’yan itatuwan. Ta haka girbinku zai ƙaru. Ni ne Ubangiji Allahnku.
26 You shall not eat with blood. You shall not practice divination, nor the observation of dreams.
“‘Kada ku ci wani abinci tare da jini a cikinsa. “‘Kada ku yi duba ko sihiri.
27 And you shall not cut the hair of your head circularly, nor shave your beard.
“‘Ba za ka aske gefe-gefe na gashin kanka ba, ko ku aske gemunku.
28 You shall not cut your flesh for the dead, and you shall not make other figures or marks on yourself. I am the Lord.
“‘Kada ku tsattsaga jikunanku saboda matattu, ba kuwa za ku yi wa kanku zāne-zāne a jiki ba. Ni ne Ubangiji.
29 Do not prostitute your daughter, lest the land be contaminated and filled with crimes.
“‘Kada ka ƙasƙantar da’yarka ta wurin mai da ita karuwa, in ba haka ba ƙasar za tă juya ga karuwanci tă kuma cika da mugunta.
30 Observe my Sabbaths, and be apprehensive toward my Sanctuary. I am the Lord.
“‘Ku kiyaye Asabbacina, ku kuma girmama wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji.
31 Do not turn aside to astrologers, nor consult with soothsayers, so as to be polluted through them. I am the Lord your God.
“‘Kada ku juya ga masu duba, ko ku nemi shawarar bokaye, gama za ku ƙazantu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji Allahnku.
32 Rise up in the presence of a gray-haired head, and honor the reputation of an elder, and fear the Lord your God. I am the Lord.
“‘Ku miƙe tsaye a gaban tsofaffi, ku nuna bangirma ga waɗanda suka tsufa, ku kuma girmama Allahnku. Ni ne Ubangiji.
33 If a newcomer lives in your land and abides among you, do not reproach him,
“‘Sa’ad da baƙo yana zama tare da ku a ƙasarku, kada ku wulaƙanta shi.
34 but let him be among you like one native born. And you shall love him as yourselves. For you were also newcomers in the land of Egypt. I am the Lord your God.
Dole ku ɗauki baƙon da yake zama tare da ku kamar haifaffe ɗan ƙasa. Ku ƙaunace shi kamar kanku, gama dā ku ma baƙi ne a Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.
35 Do not be willing to accomplish iniquity in judgment, in lengths, in weights, in quantities.
“‘Kada ku yi amfani da mudun ƙarya sa’ad da kuke awon tsawo, nauyi, ko yawan abu.
36 Let the scales be just and the weights equal, let the dry measure be just and the liquid measure be equal. I am the Lord your God, who led you away from the land of Egypt.
Ku yi amfani da ma’auni na gaskiya da mudu na gaskiya, da kuma magwaji na gaskiya. Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar.
37 Keep all my precepts, and all my judgments, and accomplish them. I am the Lord.
“‘Ku kiyaye dukan farillaina da kuma dukan dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.’”

< Leviticus 19 >