< Leviticus 10 >

1 And the sons of Aaron, Nadab and Abihu, picking up their censers, placed fire in them and incense upon them, offering in the sight of the Lord a strange fire, such as was not instructed of them.
’Ya’yan Haruna maza, Nadab da Abihu suka ɗauki farantansu, suka sa wuta a ciki, suka zuba turare a kai; suka kuma miƙa haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji, ba irin wadda Ubangiji ya umarta ba.
2 And fire coming out from the Lord destroyed them, and they died in the sight of the Lord.
Sai wuta ta fito daga Ubangiji ta cinye su, suka kuma mutu a gaban Ubangiji.
3 And Moses said to Aaron: “This is what the Lord has spoken: ‘I will be sanctified in those who approach me, and I will be glorified in the sight of all the people.’” And upon hearing this, Aaron was silent.
Sai Musa ya ce Haruna, “Ga abin da Ubangiji yake nufi sa’ad da ya ce, “‘A cikin waɗanda suka kusace ni za a tabbata ni mai tsarki ne; a fuskar dukan mutane za a kuwa girmama ni.’” Haruna ya yi shiru.
4 Then Moses called Mishael and Elzaphan, the sons of Uzziel, the paternal uncle of Aaron, and he said to them, “Go and take your brothers from the sight of the Sanctuary, and carry them beyond the camp.”
Sai Musa ya kira Mishayel da Elzafan,’ya’yan Uzziyel kawun Haruna, ya ce musu, “Ku zo nan; ku ɗauki’yan’uwanku waje da sansani, daga gaban wuri mai tsarki.”
5 And moving quickly, they took them as they lay, vested with linen tunics, and cast them outside, just as had been commanded them.
Sai suka zo suka ɗauke su, suna nan cikin taguwoyinsu, zuwa waje da sansani yadda Musa ya umarta.
6 And Moses said to Aaron, and to his sons, Eleazar and Ithamar: “Do not uncover your heads, and do not rend your garments, lest perhaps you may die, and indignation may rise up over the entire assembly. Let your brothers, and all the house of Israel, bewail the burning that the Lord has kindled.
Sa’an nan Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza, “Kada ku bar gashin kanku barkatai, kada kuma ku yage tufafinku, don kada ku mutu. Yin haka zai jawo fushin Ubangiji a kan dukan jama’a. Amma dangoginku, wato, dukan Isra’ilawa, suna iya kuka saboda waɗanda Ubangiji ya hallaka da wuta.
7 But you shall not depart from the door of the tabernacle; otherwise, you shall perish. For certainly the oil of holy anointing is upon you.” And they did all things according to the precept of Moses.
Kada ku bar ƙofar Tentin Sujada ko kuwa ku mutu, domin man Shafan Ubangiji yana kanku.” Saboda haka suka yi kamar yadda Musa ya faɗa.
8 The Lord also said to Aaron:
Sa’an nan Ubangiji ya yi magana da Haruna ya ce,
9 “You shall not drink wine, nor anything that is able to inebriate you or your sons, when you enter into the tabernacle of the testimony, lest you die. For it is an everlasting precept in your generations.
“Kai da’ya’yanka maza, ba za ku sha ruwan inabi ko wani abu mai sa jiri ba a duk sa’ad da za ku shiga cikin Tentin Sujada, in ba haka ba za ku mutu. Wannan dawwammamiyar farilla ce wa tsararraki masu zuwa.
10 And so may you have the knowledge to discern between holy and profane, between polluted and clean.
Dole ku bambanta tsakanin mai tsarki da marar tsarki, tsakanin marar tsabta da mai tsabta,
11 And so may you teach the sons of Israel all my ordinances, which the Lord has spoken to them by the hand of Moses.”
za ku kuma koyar da Isra’ilawa dukan farillan da Ubangiji ya ba su ta wurin Musa.”
12 And Moses spoke to Aaron, and to his sons, Eleazar and Ithamar, who were remaining: “Take the sacrifice which remains from the oblation of the Lord, and eat it without leaven next to the altar, because it is the Holy of holies.
Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza da suka ragu, “Ku ɗauki ragowar hadaya ta gari wadda aka yi hadaya ta ƙonawa da ita ga Ubangiji ku ci ba tare da yisti ba, a gefen bagaden, gama tsattsarka ne.
13 For you shall eat it in a holy place, which is given to you and to your sons, from the oblations of the Lord, just as has been instructed me.
Ku ci shi a tsattsarkan wuri, gama rabonka ne da na’ya’yanka daga cikin hadayun da akan ƙone da wuta ga Ubangiji; gama haka aka umarce ni.
14 Likewise, the breast which is offered, and the shoulder which is separated, you shall eat in a most clean place, you and your sons, and your daughters with you. For these have been set aside for you and your children from the victims which benefit the sons of Israel.
Amma kai da’ya’yanka maza da mata za su iya ci ƙirjin da aka kaɗa, da kuma cinyar da aka miƙa. Ku ci su a wuri mai tsabta; an ba da su gare ku da kuma’ya’yanku a matsayin rabo daga hadaya ta salama ta Isra’ilawa.
15 Since they have lifted up in the sight of the Lord, the shoulder, and the breast, and the fat that is burned on the altar, these also belong to you and to your sons as a perpetual law, just as the Lord has instructed.”
Cinyar da aka miƙa da kuma ƙirjin da aka kaɗa, dole a kawo su tare da ɓangarori kitsen hadayun da aka yi ta wuri wuta, don a kaɗa a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa. Wannan zai zama na kullayaumi gare ka da’ya’yanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
16 Meanwhile, when Moses was searching for the he-goat, which had been offered for sin, he discovered it burned up. And being angry against Eleazar and Ithamar, the sons of Aaron who were remaining, he said:
Sa’ad da Musa ya nemi sani game da akuyar hadaya don zunubi, ya kuwa gane cewa an ƙone shi, sai ya yi fushi da Eleyazar da kuma Itamar,’ya’yan Haruna maza da suka ragu, ya kuma yi tambaya,
17 “Why did you not eat the sacrifice for sin in the holy place, which is the Holy of holies, and which was given to you, so that you might carry the iniquity of the people, and might pray for them in the sight of the Lord,
“Me ya sa ba ku ci hadaya don zunubi a cikin wuri mai tsarki ba? Mafi tsaki ne; an ba ku ne don a ɗauke laifin jama’a ta wurin yin kafara saboda su a gaban Ubangiji.
18 especially since none of its blood has been brought into the holy places, and since you should have eaten it in the Sanctuary, as was instructed me?”
Da yake ba a kai jininsa cikin wuri mai tsarki ba, ya kamata ku ci akuyar a wuri mai tsarki, kamar yadda na umarta.”
19 Aaron responded: “This day, the victim for sin has been offered, and the holocaust in the sight of the Lord. But you see what has happened to me. How could I eat it, or please the Lord in the ceremonies, having a sorrowful mind?”
Sai Haruna ya amsa wa Musa, “Yau sun miƙa hadayarsu don zunubi da kuma hadayarsu ta ƙonawa a gaban Ubangiji, ga kuma irin waɗannan abubuwa da suka same ni, da a ce na ci hadaya don zunubi yau, da zai yi kyau ke nan a gaban Ubangiji?”
20 But when Moses had heard this, he was satisfied.
Da Musa ya ji haka, sai ya gamsu.

< Leviticus 10 >