< Lamentations 5 >

1 Remember, O Lord, what has befallen us. Consider and look kindly upon our disgrace.
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2 Our inheritance has been turned over to foreigners; our houses to outsiders.
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
3 We have become orphans without a father; our mothers are like widows.
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
4 We paid for our drinking water. We acquired our wood for a price.
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5 We were dragged by our necks. Being weary, no rest was given to us.
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6 We have given our hand to Egypt and to the Assyrians, so that we may be satisfied with bread.
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7 Our fathers have sinned, and are not. And we have carried their iniquities.
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8 Servants have become rulers over us. There was no one to redeem us from their hand.
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
9 We obtained our bread at the risk of our lives, before the face of the sword, in the wilderness.
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10 Our skin was burned, as if by an oven, before the face of the tempest of the famine.
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
11 They humiliated the women in Zion and the virgins in the cities of Judah.
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
12 The leaders were suspended by their hand. They were not ashamed before the faces of the elders.
An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
13 They have sexually abused the adolescents, and the children were corrupted in the wood.
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
14 The elders have ceased from the gates, the youths from the choir of the psalms.
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
15 The gladness of our heart has failed, our singing has been turned into mourning.
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16 The crown has fallen from our head. Woe to us, for we have sinned.
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
17 Because of this, our heart became gloomy; for this reason, our eyes have been darkened:
Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
18 because of mount Zion, because it was ruined. Foxes have wandered upon it.
gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
19 But you, O Lord, shall remain for eternity, your throne from generation to generation.
Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
20 Why would you forget us forever? Why would you forsake us for a long time?
Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
21 Convert us, O Lord, to you, and we shall be converted. Renew our days, as from the beginning.
Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
22 But you have utterly rejected us; you are vehemently angry against us.
sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.

< Lamentations 5 >