< Lamentations 4 >

1 ALEPH. O how the gold has become dulled, the finest color has been altered, the stones of the sanctuary have been scattered at the head of every street.
Zinariya ta rasa kyanta, hasken zinariya ya dushe! An warwatsar da tsarkakakkun duwatsu masu daraja a kan tituna.
2 BETH. The famous sons of Zion, and those clothed with the foremost gold: how they have become like earthen vessels, the work of the hands of a potter.
Dubi samarin Sihiyona masu daraja, waɗanda a dā darajarsu ta isa nauyin zinariya, yanzu ana ɗaukar su a matsayin tukwanen ƙasa, aikin maginin tukwane!
3 GHIMEL. Yet even savages expose their breast and give milk to their young. But the daughter of my people is cruel, like the ostrich in the desert.
Ko diloli suna ba’ya’yansu nono su sha, amma mutanena sun zama marasa zuciya kamar jiminai a cikin jeji.
4 DALETH. The tongue of the infant adheres to his palate out of thirst. The little ones have asked for bread, and there was no one to break it for them.
Domin ƙishirwa harshen jarirai ya manne a rufin bakinsu; yaran suna roƙo a ba su burodi, amma ba wanda ya ba su.
5 HE. Those who were fed indulgently have passed away in the roads. Those who were nourished with saffron have welcomed filth.
Waɗanda a dā sukan ci abinci mai daɗi yanzu su ne masu bara a tituna. Waɗanda a dā suke sa kaya masu kyau yanzu suna kwance a kan tarin toka.
6 VAU. And the iniquity of the daughter of my people has been made greater than the sin of Sodom, which was overthrown in a moment, and yet hands did not take captives in her.
Horon mutanena ya fi na Sodom girma, wadda aka hallaka farat ɗaya ba wani hannu da ya juya ya taimake ta.
7 ZAIN. Her Nazirites were whiter than snow, shinier than milk, more ruddy than ancient ivory, more beautiful than sapphire.
’Ya’yan sarakunansu sun fi ƙanƙara haske sun kuma fi madara fari, jikunansu sun fi murjani ja, kyansu kamar shuɗin yakutu.
8 HETH. Their face has been blacked more than coals, and they are not recognized in the streets. Their skin has adhered to their bones; it dried out and became like wood.
Amma yanzu sun fi dare duhu; ba a iya gane su a tituna. Fatar jikinsu ta manne da ƙasusuwansu; sun bushe kamar itace.
9 TETH. It was better for those slain by the sword, than for those put to death by famine. For these waste away, being consumed by the sterility of the land.
Gara waɗanda aka kashe su da takobi da waɗanda suke mutuwa da yunwa; sun rame domin rashin abinci a gona.
10 JOD. The hands of pitiable women have boiled their sons. They became their food in the grief of the daughter of my people.
Da hannuwansu mata masu tausayi sun dafa yaransu, suka zama masu abinci sa’ad da aka hallaka mutanena.
11 CAPH. The Lord has completed his fury; he has poured out the wrath of his indignation. And he has kindled a fire in Zion, and it has devoured its foundations.
Ubangiji ya saki fushinsa; ya zuba zafin fushinsa. Ya hura wuta a Sihiyona ta kuma cinye harsashin gininta.
12 LAMED. The kings of the earth, and all the inhabitants of the world, did not believe that the adversary and the enemy would enter through the gates of Jerusalem.
Sarakunan duniya ba su gaskata ba, haka ma mutanen duniya, cewa magabta da maƙiya za su iya shiga ƙofofin Urushalima.
13 MEM. It is because of the sins of her prophets, and the iniquities of her priests, who have shed the blood of the just in her midst.
Amma ya faru domin zunuban annabawanta da muguntar firistocinta, waɗanda suka zub da jinin masu adalci a cikinsu.
14 NUN. They have wandered in the streets like the blind; they have been defiled with blood. And when they were not able, they held their garments.
Yanzu suna yawo barkatai a tituna kamar makafi. Sun ƙazantu da jini yadda ba wanda zai kuskura ya taɓa rigunansu.
15 SAMECH. “Go back, you polluted ones!” they cried out to them. “Go back, go away, do not touch!” Of course, they argued, and being removed, they said among the Gentiles, “He will no longer dwell among them.”
“Ku tafi! Ba ku da tsabta!” Haka mutane suke ihu suke ce musu. “Ku tashi daga nan! Ku tashi daga nan! Kada ku taɓa mu!” Sa’ad da suka gudu suna yawo, mutanen waɗansu ƙasashe suka ce, “Ba za su ci gaba da zama a nan ba.”
16 PHE. The face of the Lord has divided them. He will no longer respect them. They were not ashamed before the faces of the priests, nor did they take pity on the elderly.
Ubangiji kansa ya warwatsa su; ya daina duban su. Ba a ba firistoci girma, ba su ba dattawa gata.
17 AIN. While we were still standing, our eyes failed, expecting help for us in vain, when we looked attentively toward a nation that was not able to save.
Idanunmu sun gaji, suna ta dubawa ko taimako zai zo; mu sa ido ko za mu ga ƙasar da za tă iya taimakon mu.
18 SADE. Our footsteps have slipped on the paths of our own streets. Our end draws near. Our days have been completed, for our end has arrived.
Ana bin sawunmu, ba za mu iya tafiya kan tituna ba. Ƙarshenmu ya kusa, kwanakinmu sun ƙare, gama ƙarshenmu ya zo.
19 COPH. Our persecutors have been swifter than the eagles of the sky. They have been pursuing us above the mountains; they have lain in wait for us in the desert.
Masu fafarar mu sun fi gaggafa mai firiya a sararin sama sauri; sun fafare mu a kan duwatsu suna fakon mu a jeji.
20 RES. The spirit of our mouth, Christ the Lord, has been captured by our sins; to him, we said, “In your shadow, we will live among the Gentiles.”
Shafaffe na Ubangiji, numfashin ranmu, ya fāɗi cikin tarkonsu. Muna tunani cewa za mu iya rayuwa cikin sauran mutane a ƙarƙashin inuwarsa.
21 SIN. Be glad and rejoice, O daughter of Edom, who dwells in the Land of Uz. The cup will also pass to you; you will be inebriated as well as naked.
Ku yi murna da farin ciki, ya Diyar Edom, ke mai zama a ƙasar Uz. Amma ke ma za a ba ki kwaf; za ki bugu ki zama tsirara.
22 THAU. Your iniquity has been completed, O daughter of Zion. He will no longer send you away to captivity. He has visited your iniquity, O daughter of Edom; he has uncovered your sins.
Ya Diyar Sihiyona, hukuncinki zai ƙare; ba zai sa zaman bautarki yă yi tsayi ba. Amma ya Diyar Edom, zai hukunta zunubinki yă tona tsiraicinki.

< Lamentations 4 >