< Judges 10 >

1 After Abimelech, a leader rose up in Israel, Tola, the son of Puah, the paternal uncle of Abimelech, a man of Issachar, who lived in Shamir on mount Ephraim.
Bayan zamanin Abimelek, sai Tola ɗan Fuwa ɗan Dodo daga Issakar ya tashi don yă ceci Isra’ila. Yana zama a Shamir a ƙasar tudu ta Efraim.
2 And he judged Israel for twenty-three years, and he died and was buried at Shamir.
Ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da uku sa’an nan ya mutu, aka kuma binne shi a Shamir.
3 After him succeeded Jair, a Gileadite, who judged Israel for twenty-two years,
Bayansa kuma sai Yayir daga Gileyad, wanda ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da biyu.
4 having thirty sons sitting upon thirty young donkeys, and who were leaders of thirty cities, which from his name were called Havvoth Jair, that is, the towns of Jair, even to the present day, in the land of Gilead.
Yana’ya’ya talatin, waɗanda suke hawan jakuna talatin. Sun shugabanci birane talatin a Gileyad, har wa yau ana ce da biranen Hawwot Yayir.
5 And Jair died, and he was buried in the place which is called Kamon.
Sa’ad da Yayir ya mutu, sai aka binne shi a Kamon.
6 But the sons of Israel did evil in the sight of the Lord, joining new sins to old, and they served idols, the Baals and Ashtaroth, and the gods of Syria and Sidon, and of Moab and the sons of Ammon, and the Philistines. And they abandoned the Lord, and they did not worship him.
Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji. Suka shiga bautar Ba’al da Ashtarot, da kuma allolin Aram, allolin Sidon, allolin Mowab, Ammonawa da kuma allolin Filistiyawa. Kuma domin Isra’ilawa sun bar Ubangiji ba su ƙara bauta masa ba,
7 And the Lord, becoming angry against them, delivered them into the hands of the Philistines and the sons of Ammon.
sai ya fusata da su. Ya sayar da su ga hannun Filistiyawa da Ammonawa,
8 And they were afflicted and vehemently oppressed for eighteen years, all who were living beyond the Jordan in the land of the Amorite, which is in Gilead,
waɗanda suka fatattake su a shekarar suka kuma ragargaza su. Shekara goma sha takwas suka yi ta danne dukan Isra’ilawan da suke gabashin Urdun a Gileyad, ƙasar Amoriyawa.
9 to such a great extent that the sons of Ammon, crossing over the Jordan, laid waste to Judah and Benjamin and Ephraim. And Israel was exceedingly afflicted.
Ammonawa su ma suka haye Urdun domin su yi yaƙi da Yahuda, Benyamin da kuma gidan Efraim; Isra’ila kuwa suka kasance cikin wahala ƙwarai da gaske.
10 And crying out to the Lord, they said: “We have sinned against you. For we have forsaken the Lord our God, and we have served the Baals.”
Sa’an nan Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji, suka ce, “Mun yi maka zunubi, mun bar Allahnmu muka shiga bautar Ba’al.”
11 And the Lord said to them: “Did not the Egyptians, and the Amorites, and the sons of Ammon, and the Philistines,
Ubangiji ya ce, “Sa’ad da Masarawa, Amoriyawa, Ammonawa, Filistiyawa,
12 and also the Sidonians, and Amalek, and Canaan, oppress you, and so you cried out to me, and I rescued you from their hand?
Sidoniyawa, Amalekawa da kuma mutanen Mawon suka wulaƙanta ku kuka kuwa yi mini kuka, ban cece ku daga hannunsu ba?
13 And yet you have forsaken me, and you have worshipped foreign gods. For this reason, I will not continue to free you any more.
Amma kuka bar ni kuka bauta wa waɗansu alloli, saboda haka ni ma ba zan ƙara cece ku ba.
14 Go, and call upon the gods whom you have chosen. Let them free you in the time of anguish.”
Ku tafi ku yi wa allolin da kuka zaɓa. Bari su cece ku sa’ad da kuke cikin wahala!”
15 And the sons of Israel said to the Lord: “We have sinned. You may repay us in whatever way pleases you. Yet free us now.”
Amma Isra’ilawa suka ce wa Ubangiji, “Mu dai mun yi zunubi. Ka yi da mu abin da ka ga dama, amma muna roƙonka ka cece mu a yanzu.”
16 And saying these things, they cast out all the idols of the foreign gods from their regions, and they served the Lord God. And he was touched by their miseries.
Sa’an nan suka zubar da allolin nan daga cikinsu suka bauta wa Ubangiji. Ubangiji kuwa bai ƙara daure da azabar da Isra’ila suke sha ba.
17 And then the sons of Ammon, shouting out together, pitched their tents in Gilead. And the sons of Israel gathered together against them, and they made camp at Mizpah.
Sa’ad da aka kira Ammonawa su yi ɗamarar yaƙi, sai su kuma kafa sansani a Gileyad, Isra’ilawa kuwa suka tattaru suka kafa sansani Mizfa.
18 And the leaders of Gilead said to one another, “Whoever among us will be the first to begin to contend against the sons of Ammon, he shall be the leader of the people of Gilead.”
Shugabannin mutanen Gileyad suka cewa juna, “Duk wanda zai fara fāɗa wa Ammonawa shi zai zama shugaban duk waɗanda suke zama a Gileyad.”

< Judges 10 >