< Joshua 6 >

1 Now Jericho was closed as well as fortified, out of fear of the sons of Israel, and no one dared to depart or to enter.
Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
2 And the Lord said to Joshua: “Behold, I have given Jericho into your hand, with its king and all the strong men.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
3 Have all the warriors circle the city once each day; you shall do so for six days.
Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
4 Then, on the seventh day, the priests shall take the seven trumpets, which are used on the jubilee, and they shall precede the ark of the covenant. And you shall circle the city seven times, and the priests shall sound the trumpets.
Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
5 And when the voice of the trumpet sounds longer and with interruptions, and it increases in your ears, then all the people shall cry out together with a very great shout, and the walls of the city shall fall to the foundation, and they shall enter it, each from a place opposite where they are standing.”
Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
6 Then Joshua, the son of Nun, called the priests, and he said to them, “Take the ark of the covenant, and let seven other priests take the seven trumpets of the jubilee, and advance before the ark of the Lord.”
Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
7 He also said to the people, “Go, and circle the city, armed, preceding the ark of the Lord.”
Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
8 And when Joshua had finished his words, and the seven priests sounded the seven trumpets before the ark of the covenant of the Lord,
Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
9 and all the armed soldiers went ahead, the remainder of the common people followed the ark, and the sound of the trumpets grew louder everywhere.
Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
10 But Joshua had instructed the people, saying, “You shall not cry out, nor shall your voice be heard, and no word at all shall proceed from your mouth, until the day arrives on which I will say to you, ‘Cry out, and shout.’”
Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
11 Thus, the ark of the Lord circled the city once each day, and returning to the camp, it remained there.
Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
12 And so, with Joshua, arising in the night, the priests took the ark of the Lord,
Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
13 and seven of them took the seven trumpets, which are used in the jubilee, and they preceded the ark of the Lord, walking and sounding the trumpets. And the armed men went before them, and the remainder of the common people followed the ark, and they were blaring the trumpets.
Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
14 And they circled the city on the second day, once, and they returned to the camp. They did so for six days.
A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
15 Then, on the seventh day, rising at first light, they circled the city, just as had been ordered, seven times.
A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
16 And at the seventh circling, when the priests sounded the trumpets, Joshua said to all of Israel: “Shout! For the Lord has delivered the city to you.
A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
17 And let this city be anathema, with all the things that are within it, before the Lord. May only Rahab the harlot live, with all who are with her in the house. For she hid the messengers whom we sent.
Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
18 But you must be careful that you do not touch any of those things, as you have been instructed, for then you would be guilty of transgression, and all the camp of Israel would be under sin and would be troubled.
Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
19 But whatever gold and silver there will be, and vessels of brass or of iron, let these be consecrated to the Lord and be stored in his treasuries.”
Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
20 Therefore, with all the people shouting, and the trumpets blaring, after the voice and the sound increased in the ears of the multitude, the walls promptly fell to ruin. And each one climbed up at the place which was opposite where he was. And they seized the city.
Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
21 And they put to death all who were in it, from man even to woman, from infant even to elder. Likewise, the oxen and sheep and donkeys, they struck down with the edge of the sword.
Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
22 But Joshua said to the two men who had been sent to explore, “Enter the house of the harlot woman, and bring her out, and all the things that are hers, just as you assured her by oath.”
Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
23 And the youths entered, and they led out Rahab, and her parents, also her brothers, and all her goods and kindred, and they caused them to dwell outside the camp.
Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
24 Then they set fire to the city and all the things that were within it, except the gold and silver, and the vessels of brass or of iron, which they consecrated into the treasury of the Lord.
Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
25 Yet truly, Joshua caused Rahab the harlot, and her father’s household, and all she had, to survive. And they lived in the midst of Israel, even to the present day. For she hid the messengers, whom he had sent to explore Jericho. At that time, Joshua made an invocation, saying:
Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
26 “Cursed before the Lord is the man who will raise up and rebuild the city of Jericho! With his firstborn, may he lay its foundation, and with the last of his children, may he set up its gates.”
A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
27 And so the Lord was with Joshua, and his name was made known throughout all the land.
Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.

< Joshua 6 >