< Joshua 24 >

1 And Joshua gathered together all the tribes of Israel at Shechem, and he called those greater by birth, and the leaders and judges and teachers. And they stood in the sight of the Lord.
Yoshuwa ya tattara dukan kabilan Isra’ila a Shekem. Ya aika a kira dattawa, shugabanni, alƙalai da manyan ma’aikatan Isra’ila, suka kai kansu gaban Allah.
2 And he spoke to the people in this way: “Thus says the Lord, the God of Israel: ‘Your fathers lived, in the beginning, across the river: Terah, the father of Abraham, and Nahor. And they served strange gods.
Yoshuwa ya ce wa dukan mutanen, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Dā can, kakanninku, Tera mahaifin Ibrahim, da Nahor sun zauna a hayin Kogin Yuferites suka yi wa waɗansu alloli sujada.
3 Then I brought your father Abraham from the parts of Mesopotamia, and I led him into the land of Canaan. And I multiplied his offspring,
Amma na ɗauki mahaifinku Ibrahim, daga ƙasar da take can a hayin Kogin Yuferites, na kawo shi ƙasar Kan’ana, na kuma ba shi’ya’ya masu yawa. Na ba shi Ishaku,
4 and I gave to him Isaac. And to him, I gave again Jacob and Esau. And I gave mount Seir to Esau as a possession. Yet truly, Jacob and his sons descended into Egypt.
ga Ishaku kuwa na ba shi Yaƙub da Isuwa. Na ba Isuwa ƙasar kan tudu ta Seyir, amma Yaƙub da’ya’yansa maza suka gangara zuwa Masar.
5 And I sent Moses and Aaron, and I struck Egypt with many signs and portents.
“‘Sai na aiki Musa da Haruna, na aukar wa Masarawa annobai, ta wurin abin da na yi ne na fitar da ku.
6 And I led you and your fathers away from Egypt, and you arrived at the sea. And the Egyptians pursued your fathers with chariots and horsemen, as far as the Red Sea.
Lokacin da na fitar da iyayenku daga Masar, suka zo teku, sai Masarawa suka fafare su da kekunan yaƙi da dawakai har zuwa Jan Teku.
7 Then the sons of Israel cried out to the Lord. And he stationed a darkness between you and the Egyptians, and he led the sea over them, and he covered them. Your eyes saw all that I did in Egypt, and you lived in the wilderness for a long time.
Amma suka yi kuka ga Ubangiji don taimako, ya kuwa sa duhu ya raba tsakaninsu da Masarawa; ya sa teku ya rufe Masarawa. Kun gani da idanunku abin da na yi wa Masarawa, sa’an nan kuka zauna a jeji na tsawon lokaci.
8 And I led you into the land of the Amorite, who was living beyond the Jordan. And when they fought against you, I delivered them into your hands, and you possessed their land, and you put them to death.
“‘Na kawo ku ƙasar Amoriyawa waɗanda suke gabas da Urdun. Suka yi yaƙi da ku, amma na ba da su a hannunku, na hallaka su a gabanku, kuka kuma mallaki ƙasarsu.
9 Then Balak, the son of Zippor, the king of Moab, rose up and fought against Israel. And he sent and called for Balaam, the son of Beor, so that he might curse you.
Lokacin da Balak ɗan Ziffor, sarkin Mowab, ya yi shiri yă yaƙi Isra’ila, ya aiki Bala’am ɗan Beyor don yă la’anta ku.
10 And I was not willing to listen to him, but on the contrary, I blessed you through him, and I freed you from his hand.
Amma ban saurari Bala’am ba, saboda haka sai ya ma sa muku albarka, na kuɓutar da ku daga hannunsa.
11 And you crossed over the Jordan, and you arrived at Jericho. And the men of that city fought against you: the Amorite, and the Perizzite, and the Canaanite, and the Hittite, and the Girgashite, and the Hivite, and the Jebusite. And I delivered them into your hands.
“‘Sai kuka ƙetare Urdun kuka isa Yeriko. Mutanen Yeriko suka yi faɗa da ku, kamar yadda Amoriyawa, Ferizziyawa, Kan’aniyawa, Hittiyawa, Girgashiyawa, Hiwiyawa, da Yebusiyawa suka yi, amma na ba da su a hannunku.
12 And I sent wasps before you. And I drove them from their places, the two kings of the Amorites, but not by your sword, and not by your bow.
Na aika rina ta kore su a idonku, haka kuma sarakunan Amoriyawan nan. Ba da takobinku ko bakanku ne kuka yi haka ba.
13 And I gave you a land, in which you did not labor, and cities, which you did not build, so that you might live in them, and vineyards and olive groves, which you did not plant.’
Na ba ku ƙasar da ba ku yi wata wahala kafin ku samu ba, na ba ku kuma biranen da ba ku gina ba; kuka kuma zauna a cikinsu, kuka ci daga’ya’yan itacensu da’ya’yan zaitun da ba ku ne kuka shuka ba.’
14 Now therefore, fear the Lord, and serve him with a perfect and very sincere heart. And take away the gods that your fathers served in Mesopotamia and in Egypt, and serve the Lord.
“Yanzu, sai ku ji tsoron Ubangiji, ku bauta masa da dukan aminci. Ku zubar da allolin da kakanninku suka yi musu sujada a hayin Kogin Yuferites da kuma a Masar, ku bauta wa Ubangiji.
15 But if it seems evil to you that you would serve the Lord, a choice is given to you. Choose today what pleases you, and whom you ought to serve above all else, either the gods that your fathers served in Mesopotamia, or the gods of the Amorites, in whose land you live: but as for me and my house, we will serve the Lord.”
Amma in kuka ga ba za ku iya bauta wa Ubangiji ba, sai ku zaɓa yau wanda za ku bauta masa, ko allolin da kakanninku suka bauta musu a hayin Kogin Yuferites, ko kuma allolin Amoriyawa, waɗanda kuke zama a cikin ƙasarsu. Amma da ni da gidana, Ubangiji ne za mu bauta wa.”
16 And the people responded, and they said: “Far be it from us that we would forsake the Lord, and serve foreign gods.
Sai mutanen suka amsa suka ce, “Allah ya kiyashe mu da rabuwa da Ubangiji Allahnmu, har a ce mu bauta wa waɗansu alloli!
17 The Lord our God himself led us and our fathers away from the land of Egypt, from the house of servitude. And he accomplished immense signs in our sight, and he preserved us along the entire way by which we journeyed, and among all the people through whom we passed.
Ubangiji Allahnmu ne da kansa ya fitar da iyayenmu daga Masar, daga ƙasar bauta, ya yi manyan abubuwan al’ajabi, a idanunmu. Ya kiyaye mu cikin dukan hanyar da muka bi, da cikin ƙasashen da muka ratsa;
18 And he cast out all the nations, the Amorite, the inhabitant of the land that we entered. And so, we will serve the Lord, for he is our God.”
Ubangiji kuwa ya kore mana dukan Amoriyawa, waɗanda suke zaune a ƙasar. Don haka mu ma za mu bauta wa Ubangiji, gama shi ne Allahnmu.”
19 And Joshua said to the people: “You will not be able to serve the Lord. For he is a holy and powerful God, and he is jealous, and he will not ignore your wickedness and sins.
Yoshuwa ya ce wa mutanen, “Ba za ku iya bauta wa Ubangiji ba gama shi Allah mai tsarki ne; mai kishi kuma. Ba zai gafarta muku zunubin tawaye ba.
20 If you leave behind the Lord, and you serve foreign gods, he will turn himself, and he will afflict you, and he will overthrow you, after all the good that he has offered to you.”
In kuka juya wa Ubangiji baya, kuka bauta wa waɗansu alloli, zai juya yă kawo muku bala’i, yă hallaka ku, yă kawo ƙarshenku.”
21 And the people said to Joshua, “By no means will it be as you are saying, but we will serve the Lord.”
Amma mutanen suka ce wa Yoshuwa, “Mu dai! Za mu bauta wa Ubangiji.”
22 And Joshua said to the people, “You yourselves are witnesses, that you have chosen the Lord so that you may serve him.” And they answered, “We are witnesses.”
Yoshuwa kuwa ya ce musu, “Ku ne shaidun kanku cewa kun zaɓi ku bauta wa Ubangiji.” Suka amsa suka ce, “I, mu ne shaidun kanmu.”
23 “Now therefore,” he said, “take away strange gods from among yourselves, and incline your hearts to the Lord, the God of Israel.”
Yoshuwa ya ce musu, “Yanzu sai ku zubar da allolin da suke cikinku, ku miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila zuciyarku.”
24 And the people said to Joshua, “We will serve the Lord our God, and we will be obedient to his precepts.”
Mutanen kuma suka ce, “Za mu bauta wa Ubangiji Allahnmu, mu kuma yi masa biyayya.”
25 Therefore, on that day, Joshua struck a covenant, and he set before the people at Shechem the precepts and the judgments.
A wannan rana Yoshuwa ya yi alkawari saboda mutanen, kuma a can Shekem ya tsara musu ƙa’idodi da dokoki.
26 He also wrote all these things in the volume of the law of the Lord. And he took a very great stone, and he stationed it under the oak that was in the Sanctuary of the Lord.
Yoshuwa kuwa ya rubuta abubuwan nan a cikin Littafin Dokoki na Allah. Sa’an nan ya ɗauki babban dutse ya ajiye a ƙarƙashin itacen oak kusa da tsattsarkan wuri na Ubangiji.
27 And he said to all the people, “Lo, this stone shall be to you as a testimony, which has heard all the words of the Lord that he has spoken to you, lest perhaps, afterward, you might choose to deny it, and to lie to the Lord your God.”
Ya ce wa duka mutanen, “Ku gani! Wannan dutse zai zama mana shaida, ya ji duk maganar da Ubangiji ya yi mana, zai zama muku shaida in ba ku yi wa Allahnku gaskiya ba.”
28 And he dismissed the people, each one to their own possession.
Sai Yoshuwa ya sallami mutane, kowa ya tafi ƙasar da aka ba shi gādo.
29 And after these things, Joshua, the son of Nun, the servant of the Lord, died, being one hundred and ten years old.
Bayan waɗannan abubuwa, Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya mutu yana da shekaru ɗari da goma.
30 And they buried him within the borders of his possession at Timnath-Serah, which is situated on mount Ephraim, before the northern side of mount Gaash.
Suka kuma binne shi a ƙasarsa ta gādo, a Timnat Sera a ƙasar kan tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
31 And Israel served the Lord during all the days of Joshua, and of the elders who lived for a long time after Joshua, and who had known all the works of the Lord that he had accomplished in Israel.
Isra’ilawa kuwa sun bauta wa Ubangiji dukan kwanakin Yoshuwa, da kuma kwanakin dattawan da ya bari, da waɗanda suka ga duk abin da Ubangiji ya yi wa Isra’ila.
32 And the bones of Joseph, which the sons of Israel had brought from Egypt, they buried at Shechem, in a portion of the field that Jacob had purchased from the sons of Hamor, the father of Shechem, for one hundred young female sheep, and so it was in the possession of the sons of Joseph.
Aka kuma binne ƙasusuwan Yusuf da aka kawo daga Masar, a Shekem a wurin da Yaƙub ya saya da azurfa ɗari daga’ya’yan Hamor, babban Shekem. Wurin ya zama gādon zuriyar Yusuf.
33 Likewise, Eleazar, the son of Aaron, died. And they buried him at Gibeah, which belongs to Phinehas, his son, and which was given to him on mount Ephraim.
Eleyazar ɗan Haruna, ya mutu aka binne shi a Gibeya, wurin da aka ba ɗansa Finehas a ƙasar kan tudu ta Efraim.

< Joshua 24 >