< Joshua 23 >

1 Now a long time passed, after the Lord had given peace to Israel by subjecting all the surrounding nations. And Joshua was now old and very advanced in age.
An daɗe bayan da Ubangiji ya ba Isra’ilawa hutu daga dukan abokan gāban da suke kewaye da su. Yoshuwa kuwa ya tsufa, shekarunsa sun yi yawa,
2 Joshua called all of Israel, and those greater by birth, and the leaders and rulers and teachers, and he said to them: “I am elderly and advanced in age.
sai ya aika a kira Isra’ilawa duka, dattawansu, shugabanninsu, alƙalansu, da manyan ma’aikatansu, ya ce musu, “Na tsufa, shekaruna kuwa sun yi yawa,
3 And you yourselves discern all that the Lord your God has done with all the surrounding nations, in what manner he himself has fought for you.
ku kanku kun ga dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi da idanunku wa dukan ƙasashen nan, Ubangiji Allahnku shi ne wanda ya yi yaƙi dominku.
4 And now, since he has divided to you by lot all the land, from the eastern part of the Jordan even to the great sea, and yet many nations still remain,
Ku tuna yadda na rarraba wa kabilanku ƙasashen nan su zama naku na gādo, dukan ƙasashen da suka rage, ƙasashen da na ci da yaƙi, tsakanin Urdun da Bahar Rum a yamma.
5 the Lord your God will destroy them, and he will take them away before your face, and you shall possess the land, just as he has promised you.
Ubangiji Allahnku kansa zai kore su a madadinku. Zai fafare su a gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu, yadda Ubangiji Allah ya yi muku alkawari.
6 Even so, be strengthened and be careful that you observe all the things that have been written in the book of the law of Moses, and that you do not turn aside from them, neither to the right, nor to the left.
“Ku yi ƙarfin hali, ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan abin da aka rubuta a cikin Littafin Dokoki na Musa, ba tare da kun juya hagu ko dama ba.
7 Otherwise, after you have entered to the Gentiles, who will be among you in the future, you might swear by the name of their gods, and serve them, and adore them.
Kada ku haɗa kai da mutanen nan da suke zama cikinku; ba ruwanku da sunayen allolinsu, kada ku rantse da su. Kada kuwa ku bauta musu ko kuwa ku rusuna musu.
8 Instead, cling to the Lord your God, just as you have done even to this day.
Sai dai ku riƙe Ubangiji Allahnku da kyau, yadda kuka yi har zuwa yanzu.
9 And then the Lord God will take away, in your sight, nations that are great and very robust, and no one will be able to withstand you.
“Ubangiji ya kori manyan ƙasashe masu ƙarfi; har wa yau ba wanda ya iya cin ku da yaƙi.
10 One of you shall pursue a thousand men of the enemies. For the Lord your God himself will fight on your behalf, just as he promised.
Mutum ɗaya a cikinku ya isa yă sa mutane dubu nasu su gudu, domin Ubangiji Allahnku yana yaƙi dominku, kamar yadda ya yi alkawari.
11 Even so, be very diligent and careful in this: that you love the Lord your God.
Saboda haka sai ku kula da kanku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku.
12 But if you choose to cling to the errors of these nations that live among you, and to mix with them by marriage, and to join with them by friendship,
“Amma in kuka juya baya kuka zama abokai ga waɗanda suka ragu suke zama a cikinku a ƙasashen nan, har kuka yi auratayya da su, kuka haɗa kai da su,
13 even now, know this: that the Lord your God will not wipe them away before your face. Instead, they shall be a pit and a snare to you, and a stumbling block at your side, and stakes in your eyes, until he takes you away and scatters you from this excellent land, which he has delivered to you.
ku tabbata cewa Ubangiji Allahnku ba zai kore muku mutanen ƙasashen nan ba, sai ma su zama muku dutsen tuntuɓe da tarko, za su zama bulala a bayanku, ƙayayyuwa a idanunku, har sai kun hallaka daga wannan ƙasa mai kyau wadda Ubangiji Allahnku ya ba ku.
14 Lo, today I am entering the way of the entire earth, and you shall know with all your mind that, out of all the words that the Lord has promised to fulfill for you, not one will pass by unfulfilled.
“Yanzu na kusa barin fuskar duniyan nan. Kun sani da dukan zuciyarku, da dukan ranku cewa, Ba ko ɗaya daga cikin alkawuran da Ubangiji Allahnku ya yi, da bai cika ba. Kowane alkawari ya cika; ba ko ɗaya da bai cika ba.
15 Therefore, just as he has fulfilled in deed what he has promised, and all prosperous things have arrived, so will he bring upon you whatever evils were threatened, until he takes you away and scatters you from this excellent land, which he has delivered to you,
Kamar yadda Ubangiji Allahnku kuwa ya cika kowane alkawari mai kyau, haka ma ba zai fasa kawo muku bala’in da ya faɗi ba, sai ya hallaka ku daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba ku.
16 when you will have transgressed the covenant of the Lord your God, which he has formed with you, and will have served strange gods, and will have adored them. And then the fury of the Lord will rise up quickly and speedily against you, and you will be taken away from this excellent land, which he has delivered to you.”
In kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku wanda ya umarce ku, in kuka je kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka rusuna musu, fushin Ubangiji zai sauko a kanku, za ku kuwa hallaka da sauri daga ƙasan nan mai kyau da ya ba ku.”

< Joshua 23 >