< Joshua 20 >

1 And the Lord spoke to Joshua, saying: “Speak to the sons of Israel, and say to them:
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
2 Separate the cities of refuge, about which I spoke to you by the hand of Moses,
“Ka gaya wa Isra’ilawa su keɓe waɗansu birane su zama biranen mafaka kamar yadda na umarce ku ta wurin Musa,
3 so that anyone who will have struck down a life unintentionally may flee to them. And so, he may be able to escape from the wrath of a close relative, who is an avenger of blood.
domin idan wani ya kashe wani bisa kuskure ba da niyyar yin kisankai ba, mutumin zai iya gudu zuwa can yă fake don kada a kashe shi.
4 And when he will have fled to one of these cities, he shall stand before the gate of the city, and he shall speak to the ancients of that city, the things that prove him innocent. And so shall they receive him, and give him a place in which to live.
Lokacin da ya gudu zuwa ɗaya daga cikin biranen nan, sai yă tsaya a ƙofar birnin yă gaya wa dattawan wannan birni damuwarsa. Sa’an nan su karɓe shi su ba shi wurin zama a cikin birninsu.
5 And if the avenger of blood will have pursued him, they shall not deliver him into his hands. For he struck down his neighbor unknowingly, one who was not proven to have been his enemy two or three days before.
In mai neman yă kashe shi don ramako ya bi shi zuwa can, ba za su miƙa shi ba domin ba da niyya ya kashe wani ba, kuma ba fushi ne ya sa ya yi kisan ba.
6 And he shall live in that city, until he stands before judgment in order to render the facts of his case, and until the death of the high priest, whoever it will be in that time. Then the one who killed a man may return, and he may enter his own city and house, from which he had fled.”
Zai zauna a wannan birni har sai taron jama’a sun yi masa shari’a, kuma har sai lokacin da babban firist wanda yake aiki a lokacin ya mutu, sa’an nan zai iya koma garinsa na dā.”
7 And they decreed Kedesh in Galilee, at mount Naphtali, and Shechem, at mount Ephraim, and Kiriath-Arba, which is Hebron, at mount Judah.
Saboda haka suka keɓe Kedesh a Galili a ƙasar kan tudu ta Naftali, Shekem a ƙasar kan tudu ta Efraim, da Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar kan tudu ta Yahuda.
8 And beyond the Jordan, opposite the eastern side of Jericho, they appointed Bezer, which is situated on the plain of the wilderness of the tribe of Reuben, and Ramoth in Gilead of the tribe of Gad, and Golan in Bashan of the tribe of Manasseh.
A hayin Urdun, gabas da Yeriko, suka keɓe Bezer ta jeji a kan tudu a cikin yankin kabilar Ruben, Ramot cikin Gileyad a kabilar Gad, da Golan cikin Bashan a kabilar Manasse.
9 These cities were established for all the sons of Israel, and for the new arrivals who were living among them, so that whoever had struck down a life unintentionally might flee to these, and not die at the hand of a close relative who desires to vindicate the blood that was shed, until he should stand before the people, in order to present his case.
In wani mutumin Isra’ila ko kuma wani baƙon da yake zama a cikinsu, ya yi kisankai cikin kuskure, zai iya gudu zuwa biranen da aka keɓe, ba za a bari mai neman ramako yă kashe shi kafin jama’a su yi masa shari’a ba.

< Joshua 20 >