< Joshua 19 >

1 And the second lot went out, for the sons of Simeon by their families. And their inheritance was,
Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
2 in the midst of the possession of the sons of Judah: Beersheba, and Sheba, and Moladah,
Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
3 and Hazar-shual, Balah, and Ezem,
Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
4 and Eltolad, Bethul, and Hormah,
Eltolad, Betul, Horma,
5 and Ziklag, and Beth-marcaboth, and Hazar-susah,
Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
6 and Bethlebaoth, and Sharuhen: thirteen cities, and their villages;
Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
7 Ain and Enrimmon, and Ether and Ashan: four cities, and their villages;
Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
8 all villages around these cities, as far as Baalath-beer, the high place facing the southern region. This is the inheritance of the sons of Simeon, according to their families,
da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
9 within the possession and lot of the sons of Judah, which was greater. And for this reason, the sons of Simeon had a possession in the midst of their inheritance.
Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
10 And the third lot fell to the sons of Zebulun, by their families; and the limit of their possession was set as far as Sarid.
Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
11 And it ascends from the sea and from Mareal. And it passes on to Dabbesheth, as far as the torrent, which is opposite Jokneam.
Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
12 And it turns back from Sarid, to the east, to the end of Chisloth-tabor. And it goes out to Daberath, and it ascends opposite Japhia.
Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
13 And from there, it continues to the eastern region of Gathhepher and Ethkazin. And goes out to Rimmon, Amthar, and Neah.
Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
14 And it circles to the north at Hannathon. And its exits are at the Valley of Iphtahel;
A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
15 and Kattath and Nahalal, and Shimron and Idalah, and Bethlehem: twelve cities, and their villages.
Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
16 This is the inheritance of the tribe of the sons of Zebulun, by their families, the cities and their villages.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
17 The fourth lot went out to Issachar, by their families.
Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
18 And his inheritance was: Jezreel, and Chesulloth, and Shunem,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
19 and Hapharaim, and Shion, and Anaharath,
Hafarayim, Anaharat,
20 and Rabbith and Kishion, Ebez
Rabbat, Kishiyon, Ebez,
21 and Remeth, and Engannim, and Enhaddah, and Bethpazzez.
Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
22 And its limit reaches to Tabor and Shahazumah and Beth-shemesh; and its exits shall be at the Jordan: sixteen cities, and their villages.
Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
23 This is the possession of the sons of Issachar by their families, the cities and their villages.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
24 And the fifth lot fell to the tribe of the sons of Asher, by their families.
Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
25 And their border was: Helkath, and Hali, and Beten, and Achshaph,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
26 and Allammelech, and Amad, and Mishal. And it extends even to Carmel by the sea, and Shihor, and Libnath.
Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
27 And it turns back toward the east at Bethdagon. And it continues on as far as Zebulun and the Valley of Iphtahel, toward the north, at Beth-emek and Neiel. And it goes out to the left of Cabul,
Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
28 and to Ebron, and Rehob, and Hammon, and Kanah, as far as the great Sidon.
ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
29 And it turns back at Ramah, even to the very fortified city of Tyre, and even to Hosah. And its exits shall be at the sea, from the lot of Achzib;
Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
30 and Ummah, and Aphek, and Rehob: twenty-two cities, and their villages.
Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
31 This is the possession of the sons of Asher, by their families, and the cities and their villages.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
32 The sixth lot fell to the sons of Naphtali, by their families.
Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
33 And its border begins from Heleph and Elon, into Zaanannim, and Adami, which is Nekeb, and Jabneel, as far as Lakkum. And its exits are as far as the Jordan.
Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
34 And the border turns back to the west at Aznoth-tabor, and it goes out from there to Hukkok. And continues on to Zebulun, in the south, and to Asher, in the west, and to Judah, at the Jordan, toward the rising of the sun.
Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
35 And the most fortified cities are Ziddim, Zer and Hammath, and Rakkath, and Chinnereth,
Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
36 and Adamah and Ramah, Hazor
Adama, Rama, Hazor,
37 and Kedesh and Edrei, Enhazor
Kedesh, Edireyi, En Hazor,
38 and Yiron and Migdalel, Horem and Bethanath, and Beth-shemesh: nineteen cities, and their villages.
Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
39 This is the possession of the tribe of the sons of Naphtali, by their families, the cities and their villages.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
40 The seventh lot went out to the tribe of the sons of Dan, by their families.
Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
41 And the border of their possession was Zorah, and Eshtaol, and Ir-shemesh, that is, the City of the Sun,
Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
42 Sha-alabbin, and Aijalon, and Ithlah,
Shalim, Aiyalon, Itla,
43 Elon, and Timnah, and Ekron,
Elon, Timna, Ekron,
44 Eltekeh, Gibbethon and Baalath,
Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
45 and Jehud, and Bene and Berak, and Gath-Rimmon,
Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
46 and Mejarkon and Rakkon, with a border that looks toward Joppa,
Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
47 and there the last part is concluded. And the sons of Dan ascended and fought against Leshem, and they seized it. And they struck it with the mouth of the sword, and they possessed it, and they lived in it, calling it by the name of Leshem-Dan, according to the name of their father Dan.
(Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
48 This is the possession of the tribe of the sons of Dan, by their families, the cities and their villages.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
49 And when he had completed dividing the land by lot to each one by their tribes, the sons of Israel gave a possession to Joshua, the son of Nun, in their midst,
Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
50 in accord with the precept of the Lord, the city he requested, Timnath-Serah, on mount Ephraim. And he built up the city, and he lived in it.
yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
51 These are the possessions which Eleazar, the priest, and Joshua, the son of Nun, and the leaders of the families and tribes of the sons of Israel divided by lot at Shiloh, before the Lord, at the door of the Tabernacle of the Testimony. And so did they divide the land.
Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.

< Joshua 19 >