< Joshua 15 >

1 And so, the lot of the sons of Judah, by their families, was this: from the border of Edom, to the desert of Sin toward the south, and even to the furthest part of the southern region.
An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.
2 Its beginning was from the summit of the very salty sea, and from its bay, which looks toward the south.
Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,
3 And it extends toward the ascent of the Scorpion, and it passes on to Sinai. And it ascends into Kadesh-barnea, and it passes through to Hezron, ascending to Addar, and encompassing Karka.
zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.
4 And from there, it passes on to Azmon, and reaches to the torrent of Egypt. And its boundary shall be the great sea; this shall be the limit of the southern region.
Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.
5 Yet truly, toward the east, the beginning shall be the very salty sea, even to the limit of the Jordan, and that which looks toward the north, from the bay of the sea, even to the same river Jordan.
Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,
6 And the border ascends into Beth-hoglah, and it crosses from the north into Beth-Arabah, ascending to the stone of Bohan, the son of Reuben.
wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
7 And it reaches as far as the borders of Debara, from the Valley of Achor, to the north, looking toward Gilgal, which is opposite the Ascent of Adummim, on the southern part of the torrent. And it crosses the waters that are called the Fountain of the Sun. And its exit shall be at the Fountain of Rogel.
Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.
8 And it ascends by the steep valley of the son of Hinnom, from the side of the Jebusite, toward the south; this is Jerusalem. And from there, it raises itself to the top of the mountain, which is opposite Geennom to the west, at the top of the Valley of the Rephaim, to the north.
Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
9 And it passes through, from the top of the mountain, even to the fountain of the Water of Nephtoah. And it continues on, as far as the villages of mount Ephron. And it inclines toward Baalah, which is Kiriath-jearim, that is, the City of Forests.
Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).
10 And it circles from Baalah, to the west, as far as mount Seir. And it passes by the side of mount Jearim, to the north, into Chesalon. And it descends into Beth-shemesh, and it passes through to Timnah.
Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.
11 And it continues on, toward the north, to a region beside Ekron. And it inclines toward Shikkeron, and it crosses to mount Baalah. And it extends into Jabneel, and the last part closes at the west with the great sea.
Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.
12 These are the borders of the sons of Judah, in their families, on all sides.
Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.
13 Yet truly, to Caleb, the son of Jephunneh, he gave a portion in the midst of the sons of Judah, just as the Lord had instructed him: the City of Arba, the father of Anak, which is Hebron.
Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)
14 And Caleb destroyed from it the three sons of Anak, Sheshai, and Ahiman, and Talmai, of the stock of Anak.
Daga can sai Kaleb ya kori’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.
15 And ascending further from there, he came to the inhabitants of Debir, which before was called Kiriath-Sepher, that is, the City of Letters.
Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).
16 And Caleb said, “Whoever will have struck down Kiriath-Sepher, and will have seized it, I will give to him Achsah, my daughter, as wife.”
Kaleb ya ce, “Zan ba da’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”
17 And Othniel, the son of Kenaz, the younger brother of Caleb, seized it. And he gave him Achsah, his daughter, as wife.
Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa’yarsa, ya kuwa aure ta.
18 And as they were traveling together, she was urged by her husband that she ask her father for a field. And she sighed, as she was sitting on her donkey. And Caleb said to her, “What is it?”
Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”
19 But she answered: “Give a blessing to me. You have given to me a southern and dry land; join to it also a watered land.” And so Caleb gave to her the watered land above and below it.
Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.
20 This is the possession of the tribe of the sons of Judah, by their families.
Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.
21 And the cities, from the furthest parts of the sons of Judah, beside the borders of Edom to the south, were: Kabzeel and Eder and Jagur,
Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,
22 and Kinah and Dimonah and Adadah,
Kina, Dimona, Adada,
23 and Kadesh and Hazor and Ithnan,
Kedesh, Hazor, Itnan,
24 Ziph and Telem and Bealoth,
Zif, Telem, Beyalot,
25 new Hazor and Kerioth-Hezron, which is Hazor,
Hazor-Hadatta, Keriyot Hezron (wato, Hazor),
26 Amam, Shema, and Moladah,
Amam, Shema, Molada,
27 and Hazar-gaddah and Heshmon and Bethpelet,
Hazar Gadda, Heshmon, Bet-Felet,
28 and Hazar-shual and Beersheba and Biziothiah,
Hazar Shuwal, Beyersheba, Biziyotiya,
29 and Baalah and Iim and Ezem,
Ba’ala, Iyim, Ezem,
30 and Eltolad and Chesil and Hormah,
Eltolad, Kesil, Horma,
31 and Ziklag and Madmannah and Sansannah,
Ziklag, Madmanna, Sansanna,
32 Lebaoth and Shilhim, and Ain and Rimmon. All the cities were twenty-nine, and their villages.
Lebayot, Shilhim, Ayin, Rimmon, jimillarsu, garuruwa da ƙauyukansu duka ashirin da tara ne.
33 Truly, in the plains, there were: Eshtaol and Zorah and Ashnah,
Biranen da suke a filayen kwari su ne, Eshtawol, Zora; Ashna,
34 and Zanoah and Engannim, and Tappuah and Enam,
Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,
35 and Jarmuth and Adullam, Socoh and Azekah,
Yarmut, Adullam, Soko, Azeka,
36 and Shaaraim and Adithaim, and Gederah and Gederothaim: fourteen cities, and their villages.
Sha’arayim, Aditayim, Gedera (Gederotayim ke nan). Garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.
37 Zenan and Hadashah and Middalgad,
Zenan, Hadasha, Migdal Gad,
38 Dilean and Mizpeh and Joktheel,
Dileyan, Mizfa, Yokteyel,
39 Lachish and Bozkath and Eglon,
Lakish, Bozkat, Eglon,
40 Cabbon and Lahmam and Chitlish,
Kabbon, Lahman, Kitlish,
41 and Gederoth and Bethdagon, and Naamah and Makkedah: sixteen cities, and their villages.
Gederot, Bet-Dagon, Na’ama, Makkeda, garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
42 Libnah and Ether and Ashan,
Libna, Eter, Ashan,
43 Iphtah and Ashnah and Nezib,
Yefta, Ashna, Nezib,
44 and Keilah and Achzib and Mareshah: nine cities, and their villages.
Keyila, Akzib, Maresha, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
45 Ekron, with its towns and villages:
Ekron da ƙauyukan da suke kewaye da ita;
46 from Ekron, as far as the sea, all that inclines toward Ashdod, and its villages.
yammancin Ekron da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.
47 Ashdod, with its towns and villages. Gaza, with its towns and villages, as far as the torrent of Egypt, with the great sea as its border.
Ashdod da garuruwa da kuma ƙauyukan da suke kewaye da ita, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta har zuwa Rafin Masar da kuma Bahar Rum.
48 And on the mountain, Shamir and Jattir and Socoh,
Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne, Shamir, Yattir, Soko,
49 and Dannah, and Kiriath-Sannah, which is Debir,
Danna, Kiriyat Sanna (wato, Debir),
50 Anab and Eshtemoh and Anim,
Anab, Eshtemo, Anim,
51 Goshen and Holon and Giloh: eleven cities, and their villages.
Goshen, Holon, Gilo, garuruwa goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.
52 Arab and Dumah and Eshan,
Arab, Duma, Eshan,
53 and Janim and Beth-Tappuah and Aphekah,
Yanum, Bet-Taffuwa, Afeka,
54 Humtah and Kiriath-Arba, which is Hebron, and Zior: nine cities, and their villages.
Humta, Kiriyat Arba (wato, Hebron) da Ziyor, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
55 Maon and Carmel, and Ziph and Juttah,
Mawon, Karmel, Zif, Yutta
56 Jezreel and Jokdeam and Zanoah,
Yezireyel, Yokdeyam, Zanowa,
57 Kain, Gibeah, and Timnah: ten cities, and their villages.
Kayin, Gibeya, Timna, garuruwa goma ke nan da ƙauyukansu.
58 Halhul and Bethzur and Gedor,
Halhul, Bet-Zur, Gedor,
59 Maarath and Bethanoth and Eltekon: six cities, and their villages.
Ma’arat, Bet-Anot, Eltekon, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
60 Kiriath-baal, which is Kiriath-jearim, the City of Forests, and Rabbah: two cities, and their villages.
Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim) da Rabba, garuruwa biyu ke nan da ƙauyukansu.
61 In the desert: Beth-Arabah, Middin, and Secacah,
Biranen da suke a jeji kuwa su ne, Bet-Araba, Middin, Sekaka,
62 and Nibshan, and the City of Salt, and Engedi: six cities, and their villages.
Nibshan, Birnin gishiri da En Gedi, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
63 But the sons of Judah were not able to destroy the Jebusite inhabitants of Jerusalem. And so the Jebusite lived with the sons of Judah in Jerusalem, even to the present day.
Kabilar Yahuda kuwa ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zama cikin Urushalima ba; har wa yau Yebusiyawa suna nan zaune tare da mutanen Yahuda.

< Joshua 15 >