< Joshua 13 >

1 Joshua was old and advanced in age, and the Lord said to him: “You have grown old, and are aged, and a very wide land remains, which has not yet been divided by lot,
Sa’ad da Yoshuwa ya tsufa, Ubangiji ya ce masa, “Ka tsufa ƙwarai, ga shi kuma akwai sauran ƙasa mai fāɗi da ba ku riga kun mallaka ba.
2 specifically, all of Galilee, Philistia, and all of Geshur;
“Ga ƙasar da ta rage, “dukan yankunan Filistiyawa da na Geshurawa.
3 from the muddy river, which irrigates Egypt, as far as the border of Ekron toward the north, the land of Canaan, which is divided among the rulers of Philistia: the Gazites, and the Ashdodites, the Ashkelonites, the Gathites, and the Ekronites;
Daga Kogin Shihor a gabashin Masar zuwa sashen Ekron a arewa, dukan wannan ƙasa ana lissafta ta a cikin ƙasar Kan’aniyawa, ko da yake tana a sashen da sarakuna biyar na Filistiyawa na Gaza, Ashdod, Ashkeloniyawa, Gat da Ekron; na Awwiyawa.
4 truly, to the south are the Hivites, all the land of Canaan, and Mearah of the Sidonians, as far as Aphek and the borders of the Amorite
Daga wajen kudu kuma, dukan ƙasar Kan’aniyawa ce. Iyakarta a arewa ta fara daga Ara ta Sidoniyawa har zuwa Afek, ta zarce har zuwa iyakar Amoriyawa;
5 and his confines; also, the region of Lebanon toward the east, from Baalgad, under mount Hermon, until you enter into Hamath;
da ƙasar Gebaliyawa; da dukan Lebanon wajen gabas daga Ba’al-Gad a gindin Dutsen Hermon zuwa Lebo Hamat.
6 all who live in the mountains from Lebanon, as far as the waters of Misrephoth, and all the Sidonians. I am the One who will wipe them out, before the face of the sons of Israel. Therefore, let their land become a part of the inheritance of Israel, just as I have instructed you.
“Dukan mazauna kan yankunan tuddai daga Lebanon zuwa Misrefot Mayim, wato, dukan Sidoniyawa, ni da kaina zan kore su a gaban Isra’ilawa. Ka tabbata ka raba wa Isra’ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka,
7 And now, divide the land as a possession to the nine tribes, and to the one half tribe of Manasseh.”
ka raba ta tă zama gādo wa kabilu tara da kuma rabin kabilar Manasse.”
8 With them, Reuben and Gad have possessed the land, which Moses, the servant of the Lord, delivered to them beyond the river Jordan, on the eastern side:
Rabin kabilar Manasse, mutanen Ruben da mutanen Gad suka karɓi rabonsu na gādo wanda Musa ya ba su a gabashin Urdun. Abin da Musa bawan Ubangiji ya ba su ke nan.
9 from Aroer, which is situated on the bank of the torrent Arnon and in the midst of the valley, and all the plains of Medeba, as far as Dibon;
Wannan ya tashi daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, ya kuma haɗa da ƙasar da take tudun Medeba har zuwa Dibon,
10 and all the cities of Sihon, the king of the Amorites, who reigned in Heshbon, even to the borders of the sons of Ammon;
da dukan garuruwan Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon, har zuwa iyakar Ammonawa.
11 and Gilead, as well as the borders of Geshur and Maacati, and all of mount Hermon, and all of Bashan, as far as Salecah;
Haɗe da Gileyad, inda mutanen Geshur da Ma’aka suke. Dukan Dutsen Hermon, da dukan Bashan har zuwa Saleka,
12 the entire kingdom of Og in Bashan, who reigned at Ashtaroth and Edrei, (he was among the last of the Rephaim). And Moses struck and destroyed them.
wato, dukan masarautar Og a Bashan, wanda ya yi mulkin Ashtarot da Edireyi, yana cikin waɗanda suke na ƙarshe da ba a kashe ba a cikin Refahiyawa. Musa ya ci su da yaƙi, ya ƙwace ƙasarsu.
13 And the sons of Israel were not willing to destroy Geshur and Maacati, and so they have lived in the midst of Israel, even to the present day.
Amma Isra’ilawa ba su kori mutanen Geshur da Ma’aka ba, saboda haka suka ci gaba da zama cikin Isra’ilawa har wa yau.
14 But to the tribe of Levi, he did not give a possession. Instead, the sacrifices and victims of the Lord, the God of Israel, these are his inheritance, just as he spoke to him.
Kabilar Lawiyawa ne kaɗai Musa bai ba ta gādo ba, gama hadayun ƙonawa da ake miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
15 Therefore, Moses gave a possession to the tribe of the sons of Reuben, according to their families.
Ga abin da Musa ya ba kabilar Ruben bisa ga iyalansu.
16 And their border was from Aroer, which is situated on the bank of the torrent Arnon, and in the midst of the valley of the same torrent, with all the flatlands that lead to Medeba;
Abin da ya kama daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba
17 and Heshbon, and all their villages, which are in the plains; also Dibon, and Bamothbaal, and the town of Baalmeon,
zuwa Heshbon, da dukan garuruwan kan tudu, haɗe da Dibon, Bamot Ba’al, Bet-Ba’al-Meyon,
18 and Jahaz, and Kedemoth, and Mephaath,
Yahza, Kedemot, Mefa’at,
19 and Kiriathaim, and Sibmah, and Zereth-shahar on the mountain of the steep valley;
Kiriyatayim, Sibma, Zeret Shahar kan tudu cikin kwari,
20 Bethpeor, and the descending slopes of Pisgah, and Beth-jeshimoth;
Bet-Feyor, gangaren Fisga da Bet-Yeshimot,
21 and all the cities of the plain, and all the kingdoms of Sihon, the king of the Amorites, who reigned at Heshbon, whom Moses struck down with the leaders of Midian: Evi, and Rekem, and Zur, and Hur, and Reba, the commanders of Sihon, inhabitants of the land.
dukan garuruwan da suke kan tudu da dukan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Musa ya yi nasara da shi, da shugabannin Midiyawa, wato, Ewi, Rekem, Zur, Hur, da Reba, sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar.
22 And the sons of Israel killed Balaam, the son of Beor, the seer, with the sword, along with the others who were slain.
Ƙari a kan waɗanda aka kashe a yaƙi, Isra’ilawa suka kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi don yana duba.
23 And the river Jordan was made the border of the sons of Reuben; this is the possession of the Reubenites, by their families, in cities and villages.
Gefen Urdun shi ne iyakar mutanen Ruben. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon mutanen Ruben, bisa ga iyalansu.
24 And Moses gave to the tribe of Gad and his sons, by their families, a possession, of which this is the division:
Ga abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalansu.
25 the border of Jazer, and all the cities of Gilead, and one half part of the land of the sons of Ammon, as far as Aroer, which is opposite Rabbah;
Yankin ƙasarsu ya ƙunshi Yazer, da dukan garuruwan Gileyad, da rabin ƙasar Ammonawa har zuwa Arower kusa da Rabba,
26 and from Heshbon as far as Ramath, Mizpeh, and Betonim; and from Mahanaim as far as the borders of Debir;
da kuma daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, da kuma daga Mahanayim zuwa sashen Debir,
27 also, in the valley Beth-haram and Beth-nimrah, and Succoth, and Zaphon, the remaining part of the kingdom of Sihon, the king of Heshbon; the limit of this also is the Jordan, as far as the furthest part of the sea of Chinnereth, beyond the Jordan on the eastern side.
kuma a cikin kwari, Bet-Haram, Bet-Nimra, Sukkot da Zafon da kuma sauran masarautar Sihon sarkin Heshbon (gabashin Urdun, abin da ya kama har zuwa ƙarshen Tekun Kinneret).
28 This is the possession of the sons of Gad, by their families, in their cities and villages.
Waɗannan garuruwan da ƙauyukansu duka, gādon mutanen Gad ne, bisa ga iyalansu.
29 He also gave, to the one half tribe of Manasseh and to his sons, a possession according to their families,
Ga abin da Musa ya ba rabin kabilar Manasse, wato, wa rabin zuriyar Manasse, bisa ga iyalansu.
30 the beginning of which is this: from Mahanaim, all of Bashan, and all the kingdoms of Og, the king of Bashan, and all the villages of Jair, which are in Bashan, sixty towns;
Abin da ya miƙe daga Mahanayim haɗe da dukan Bashan, da gefen masarautar Og sarkin Bashan, da dukan garuruwan Yayir guda sittin da suke a Bashan,
31 and one half part of Gilead, and Ashtaroth, and Edrei, the cities of the kingdom of Og in Bashan, to the sons of Machir, the son of Manasseh, to one half part of the sons of Machir, according to their families.
da rabin Gileyad, da Ashtarot, Edireyi (biranen sarki Og a Bashan). Wannan shi ne rabon da zuriyar Makir ɗan Manasse suka samu, domin rabin’ya’yan Makir maza, bisa ga iyalansu.
32 Moses divided this possession, in the plains of Moab, beyond the Jordan, opposite Jericho on the eastern side.
Waɗannan su ne rabon gādon da Musa ya yi lokacin da suke cikin filayen Mowab a hayin gabashin Urdun kusa da Yeriko.
33 But to the tribe of Levi he did not give a possession. For the Lord, the God of Israel, is himself their possession, just as he spoke to him.
Amma Musa bai ba kabilar Lawiyawa gādo ba; Ubangiji, Allah na Isra’ila, shi ne gādonsu kamar yadda ya yi musu alkawari.

< Joshua 13 >