< Joshua 11 >

1 And when Jabin, the king of Hazor, had heard these things, he sent to Jobab, the king of Madon, and to the king of Shimron, and to the king of Achshaph,
Sa’ad da Yabin sarkin Hazor ya ji wannan, sai ya aika saƙo zuwa wurin Yobab sarkin Madon, da sarkin Shimron, da Akshaf,
2 also to the kings of the north, who were living in the mountains, and in the plains opposite the southern region of Chinneroth, and also in the plains and the regions of Dor, beside the sea,
ya kuma aika zuwa ga sarakunan arewa waɗanda suke kan tuddai da kuma waɗanda suke cikin Araba a kudancin Kinneret da cikin filayen kwari, da cikin Nafot Dor a yamma;
3 also to the Canaanites, from east to west, and to the Amorite, and the Hittite, and the Perizzite, and the Jebusite in the mountains, also to the Hivite who was living at the base of Hermon, in the land of Mizpah.
ya kuma aika zuwa ga Kan’aniyawa a gabas da yamma; da kuma zuwa ga Amoriyawa, Hittiyawa da Ferizziyawa, da Yebusiyawa da suke kan tuddai; da kuma Hiwiyawa masu zama a gindin dutsen Hermon a yankin Mizfa.
4 And they all went forth with their troops, a people exceedingly numerous, like the sand that is on the shore of the sea. And their horses and chariots were an immense multitude.
Suka fito da dukan rundunansu da keken yaƙi masu yawan gaske, babbar runduna, yawansu ya yi kamar yashin bakin teku.
5 And all these kings assembled at the waters of Merom, so that they might fight against Israel.
Duk sarakunan nan suka haɗa mayaƙansu tare, suka kafa sansani a bakin Ruwayen Meron don su yi yaƙi da Isra’ilawa.
6 And the Lord said to Joshua: “You should not fear them. For tomorrow, at this same hour, I will deliver all these to be wounded in the sight of Israel. You will hamstring their horses, and you will burn their chariots with fire.”
Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoronsu, domin war haka gobe zan ba da dukansu a hannun Isra’ilawa, za su kuwa karkashe su. Za ku gurgunta dawakansu, ku kuma ƙone keken yaƙinsu.”
7 And Joshua, and the entire army with him, came against them suddenly, at the waters of Merom, and they rushed upon them.
Sai Yoshuwa da dukan mayaƙan suka auka musu a bakin Ruwayen Meron.
8 And the Lord delivered them into the hands of Israel. And they struck them, and they pursued them as far as the great Sidon, and the waters of Misrephoth, and the field of Mizpeh, which is toward the eastern region. He struck them all, so that nothing was left of them to remain.
Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa nasara a kan su, suka ci su da yaƙi, suka fafare su har zuwa Sidon Babba, zuwa Misrefot Mayim, har zuwa Kwarin Mizfa a gabas, ba wanda suka bari da rai.
9 And he did just as the Lord had instructed him. He hamstrung their horses, and he burned their chariots with fire.
Yoshuwa ya yi musu yadda Ubangiji ya umarta, ya gurgunta dawakansu, ya kuma ƙone keken yaƙinsu.
10 And turning back, he immediately seized Hazor. And he struck down its king with the sword. For Hazor, from antiquity, held the first position among all these kingdoms.
A lokacin nan Yoshuwa ya koma da baya ya ci Hazor da yaƙi, ya kuma kashe sarkinta da takobi. (Hazor ce babbar masarautan ƙasashen nan.)
11 And he struck down all the souls that were staying there. He did not leave in it any remains, but he destroyed everything unto utter annihilation, and he destroyed the city itself with fire.
Suka karkashe duk mazaunan ƙasar da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba, suka kuma ƙona Hazor.
12 And he seized, struck, and destroyed all the surrounding cities and their kings, just as Moses, the servant of God, had instructed him.
Yoshuwa ya ƙwace masarautun nan duka ya kuma kashe sarakunansu da takobi, ya hallakar da su ƙaƙaf kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarta.
13 And except for the cities that were on hills and in elevated places, the rest Israel burned. One only, highly-fortified Hazor, was consumed with fire.
Duk da haka Isra’ilawa ba su ƙone biranen da suke kan tuddai ba, sai Hazor kaɗai Yoshuwa ya ƙone.
14 And the sons of Israel divided among themselves all the plunder of these cities, and the cattle, putting to death all persons.
Isra’ilawa suka kwashi ganima da dabbobi na waɗannan birane, amma suka karkashe mutanen duka da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba.
15 Just as the Lord had instructed his servant Moses, so did Moses instruct Joshua, and he fulfilled everything. He did not omit even one word out of all the commandments, which the Lord had commanded Moses.
Yadda Ubangiji ya umarci bawansa Musa, haka Musa ya umarci Yoshuwa, shi kuwa ya yi duk abin da Ubangiji ya umarci Musa.
16 And so Joshua seized the entire land of the mountains, and of the south, and the land of Goshen, and the plains, and the western region, and the mountain of Israel, and its plains.
Saboda haka Yoshuwa ya cinye ƙasar duka da yaƙi, dukan Negeb, duka yankin Goshen, filayen kwari na yamma, Araba da tuddai na Isra’ila da kwarinta.
17 As for the part of the mountain that ascends to Seir, as far as Baalgad, along the plain of Lebanon under mount Hermon, all their kings he seized, struck down, and killed.
Daga Dutsen Halak wanda ya miƙe zuwa wajajen Seyir, zuwa Ba’al-Gad a Kwarin Lebanon ƙasa da Dutsen Hermon. Ya kama sarakunansu ya karkashe su.
18 For a long time, Joshua fought against these kings.
Yoshuwa ya daɗe yana yaƙi da dukan waɗannan sarakuna.
19 There was not a city that delivered itself to the sons of Israel, except the Hivites who were living at Gibeon. For he seized it all in warfare.
Sai Hiwiyawa kaɗai waɗanda suke zama a Gibeyon, sauran ba ko birni ɗaya da ta yi yarjejjeniya ta salama da Isra’ilawa, Isra’ilawa kuwa suka ci dukansu da yaƙi.
20 For it was the sentence of the Lord that their hearts would be hardened, and that they would fight against Israel and fall, and that they did not deserve any clemency, and that they should perish, just as the Lord had commanded Moses.
Gama Ubangiji ne ya taurare zukatansu waɗannan sarakuna suka yi yaƙi da Isra’ilawa don yă hallaka su gaba ɗaya, yă gamar da su ba jinƙai, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
21 In that time, Joshua went and put to death the Anakim from the mountains, from Hebron and Debir and Anab, and from all the mountains of Judah and Israel. And he destroyed their cities.
A lokacin nan Yoshuwa ya je ya hallaka Anakawa daga ƙasar tudu. Daga Hebron, Debir da Anab. Daga dukan ƙasar tuddai na Yahuda, da kuma dukan ƙasar tudu ta Isra’ila, Yoshuwa ya hallaka su duka da garuruwansu.
22 He did not leave any from the stock of the Anakim in the land of the sons of Israel, except the cities of Gaza, and Gath, and Ashdod, which alone were left behind.
Ba a bar waɗansu Anakawa a harabar Isra’ila ba; sai dai a Gaza, Gat da Ashdod ne aka samu waɗanda suka ragu da rai.
23 Thus, Joshua seized all the land, just as the Lord spoke to Moses, and he delivered it as a possession to the sons of Israel, according to their divisions and tribes. And the land rested from battles.
Yoshuwa kuwa ya ƙwace dukan ƙasar yadda Ubangiji ya umarci Musa, ya ba da ita ta zama ƙasar gādo ga Isra’ilawa, kabila-kabila. Ta haka ƙasar ta huta daga yaƙi.

< Joshua 11 >