< Joshua 1 >

1 And after the death of Moses, the servant of the Lord, it happened that the Lord spoke to Joshua, the son of Nun, the minister of Moses, and he said to him:
Bayan mutuwar Musa bawan Ubangiji, sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa ɗan Nun, mataimakin Musa,
2 “Moses, my servant, has died. Rise up, and cross this Jordan, you and all the people with you, into the land which I will give to the sons of Israel.
“Bawana Musa ya mutu. Yanzu sai ka tashi tare da mutanen nan duka, ku yi shirin ƙetare kogin Urdun zuwa cikin ƙasar da zan ba su Isra’ilawa.
3 I will deliver to you every place that the step of your foot will tread upon, just as I said to Moses.
Zan ba ku duk ƙasar da za ku taka, kamar yadda na yi wa Musa alkawari.
4 From the desert and from Lebanon, even to the great river Euphrates, all the land of the Hittites, as far as the great sea opposite the setting of the sun, shall be your border.
Ƙasar da ta kama daga hamada zuwa Lebanon, zuwa babban Kogin, wato, Kogin Yuferites, da dukan ƙasar Hittiyawa zuwa Bahar Rum, wajen yamma.
5 No one will be able to resist you during all the days of your life. Just as I was with Moses, so will I be with you. I will not leave you, nor will I forsake you.
Ba wanda zai yi tsayayya da kai dukan kwanakin ranka. Yadda na kasance tare da Musa, haka zan kasance tare da kai; ba zan taɓa rabuwa da kai ba; ba zan yashe ka ba.
6 Be strengthened and be steadfast. For you shall divide by lot, to this people, the land about which I swore to their fathers that I would deliver it to them.
“Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, gama kai za ka bi da mutanen nan har su karɓi ƙasar da na yi wa kakanninsu alkawari zan ba su.
7 Therefore, be strengthened and be very steadfast, so that you may observe and accomplish the entire law, which Moses, my servant, instructed to you. You may not turn aside from it to the right, nor to the left. So may you understand all that you should do.
Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, ka yi lura fa, ka yi biyayya da dokokin da bawana Musa ya ba ka; kada ka kauce ga bin dokokin ko hagu ko dama, domin ka yi nasara a duk, inda za ka je.
8 The book of this law shall not depart from your mouth. Instead, you shall meditate upon it, day and night, so that you may observe and do all the things that are written in it. Then you shall direct your way and understand it.
Kada ka bar Littafin Dokokin nan yă rabu da bakinka, sai dai ka yi ta tunani game da shi dare da rana, don ka lura, ka yi duk abin da aka rubuta a ciki, ta haka ne za ka yi nasara cikin duk abin da za ka yi.
9 Behold, I am instructing you. Be strengthened, and be steadfast. Do not dread, and do not fear. For the Lord your God is with you in all things, wherever you may go.”
Ba ni na umarce ka ba? Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro. Kada ka ji tsoro; kada ka karaya, gama Ubangiji Allahnka zai kasance tare da kai duk inda za ka je.”
10 And Joshua instructed the leaders of the people, saying: “Cross through the midst of the camp, and command the people, and say:
Saboda haka sai Yoshuwa ya umarci shugabannin mutane,
11 ‘Prepare your food supplies. For after the third day, you shall cross the Jordan, and you shall enter so as to possess the land, which the Lord your God will give to you.’”
“Ku ratsa cikin sansani, ku gaya wa mutane, ‘Ku shirya guzurinku. Nan da kwana uku za ku ƙetare Urdun a nan, don ku je ka mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ta zama taku.’”
12 Likewise, he said to the Reubenites and to the Gadites, and to the one half tribe of Manasseh:
Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse,
13 “Remember the words, which Moses, the servant of the Lord, instructed to you, saying: ‘The Lord your God has given you rest, and has given you all the land.’
“Ku tuna da umarnin da Musa bawan Ubangiji ya yi muku. ‘Ubangiji Allahnku ya ba ku hutawa, ya kuma ba ku wannan ƙasa.’
14 Your wives and sons, as well as the cattle, shall remain in the land which Moses delivered to you beyond the Jordan. But as for you, pass over with weapons, before your brothers, all you who are strong of hand, and fight on their behalf,
Matanku, da yaranku, da kuma dabbobinku za su kasance a ƙasar da Musa ya ba ku a gabashin Urdun, amma dole mayaƙanku, su yi shirin yaƙi su haye, su yi gaba tare da’yan’uwanku, za ku taimaki’yan’uwanku
15 until the Lord gives rest to your brothers, just as he has given to you, and until they also possess the land, which the Lord your God will give to them. And so shall you be returned to the land of your possession. And you shall live in the land, which Moses, the servant of the Lord, gave to you beyond the Jordan, opposite the rising of the sun.”
har sai lokacin da Ubangiji ya ba su hutawa, kamar yadda ya yi muku, kuma har sai su ma sun ƙwace ƙasar da Ubangiji Allahnku ya yi alkawari zai ba su. Bayan haka ne za ku koma ku mallaki ƙasarku, wadda Musa bawan Ubangiji ya ba ku a gabashin Urdun.”
16 And they responded to Joshua, and they said: “All that you have instructed to us, we shall do. And wherever you will send us, we shall go.
Sai suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “Duk abin da ka ce mu yi, za mu yi. Duk inda kuma ka aike mu, za mu je.
17 Just as we obeyed Moses in all things, so shall we obey you also. But may the Lord your God be with you, just as he was with Moses.
Kamar yadda muka yi wa Musa biyayya, haka za mu yi maka biyayya. Ubangiji Allahnka ya kasance tare da Musa.
18 Whoever will contradict your mouth, and whoever will not obey all of your words, which you will instruct to him, let him die. But may you be strengthened, and may you act manfully.”
Duk wanda ya yi wa maganarka tawaye, ya ƙi yă yi biyayya da maganarka, ko da umarnin da ka ba shi, za a kashe shi. Ka dai ƙarfafa ka kuma yi ƙarfi hali!”

< Joshua 1 >