< Jonah 3 >

1 And the word of the Lord came to Jonah a second time, saying:
Sa’an nan sai maganar Ubangiji ta zo wa Yunana sau na biyu.
2 Rise, and go to Nineveh, the great city. And preach in it the preaching that I say to you.
“Tafi babban birnin nan Ninebe, ka yi masa shelar saƙon da na ba ka.”
3 And Jonah rose, and he went to Nineveh in accordance with the word of the Lord. And Nineveh was a great city of three days’ journey.
Sai Yunana ya yi biyayya da maganar Ubangiji, ya tafi Ninebe. Ninebe birni ne da yake da muhimmanci, wanda sai an ɗauki kwana uku kafin a iya zaga shi.
4 And Jonah began to enter into the city one day’s journey. And he cried out and said, “Forty days more and Nineveh shall be destroyed.”
A rana ta fari, Yunana ya kama tafiya yana ratsa birnin. Sai ya yi shela cewa, “Nan da kwana arba’in za a hallaka Ninebe?”
5 And the men of Nineveh believed in God. And they proclaimed a fast, and they put on sackcloth, from the greatest all the way to the least.
Mutanen Ninebe kuwa suka gaskata Allah. Aka yi shela a yi azumi, sai dukansu daga babba har zuwa ƙaraminsu, suka sa tufafin makoki.
6 And word reached the king of Nineveh. And he rose from his throne, and he threw off his robe from himself and was clothed in sackcloth, and he sat in ashes.
Da saƙon Yunana ya kai kunnen sarkin Ninebe, sai ya tashi daga kujerar mulkinsa, ya tuɓe alkyabbarsa, ya sa rigar makoki, ya zauna cikin toka.
7 And he cried out and spoke: “In Nineveh, from the mouth of the king and of his princes, let it be said: Men and beasts and oxen and sheep may not taste anything. Neither shall they feed or drink water.
Sai ya yi umarni a Ninebe cewa, “Bisa ga umarnin sarki da fadawansa. “Kada a bar wani mutum ko dabba, garke ko shannu, su ɗanɗana wani abu; kada a bari su ci ko su sha.
8 And let men and beasts be covered with sackcloth, and let them cry out to the Lord with strength, and may man be converted from his evil way, and from the iniquity that is in their hands.
Bari kowane mutum da dabba yă yafa rigunan makoki. Kowa yă roƙi Allah da gaske, kowa kuma yă bar mugayen ayyukan da yake yi.
9 Who knows if God may turn and forgive, and may turn away from his furious wrath, so that we might not perish?”
Wa ya sani? Ko Allah zai ji tausayinmu da kuma juyayinmu yă janye zafin fushinsa don kada mu hallaka.”
10 And God saw their works, that they had been converted from their evil way. And God took pity on them, concerning the harm that he had said he would do to them, and he did not do it.
Da Allah ya ga abin da suka yi, da kuma yadda suka juya daga mugayen hanyoyinsu sai ya ji tausayinsu, bai kawo hallaka a kansu yadda ya yi shirin yi ba.

< Jonah 3 >