< John 12 >

1 Then six days before the Passover, Jesus went to Bethania, where Lazarus had died, whom Jesus raised up.
Kwana shidda kafin idin ketarewa, Yesu ya zo Baitanya inda Li'azaru yake, wato wannan da Yesu ya tada daga matattu.
2 And they made a dinner for him there. And Martha was ministering. And truly, Lazarus was one of those who were sitting at table with him.
Sai suka shirya masa abinci a wurin kuma Matta ce ke hidima, Li'azaru kuwa ya kasance cikin wadanda ke kan tebiri tare da Yesu.
3 And then Mary took twelve ounces of pure spikenard ointment, very precious, and she anointed the feet of Jesus, and she wiped his feet with her hair. And the house was filled with the fragrance of the ointment.
Sai Maryamu ta dauki wani turare da aka yi da man nard, ta shafe kafafun Yesu da shi, ta kuma share kafafun nasa da gashin kanta. Sai gida ya cika da kamshin turaren.
4 Then one of his disciples, Judas Iscariot, who was soon to betray him, said,
Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin almajiransa, wanda zai bashe shi, ya ce, “
5 “Why was this ointment not sold for three hundred denarii and given to the needy?”
“Me yasa ba a sayar da wannan turare dinari dari uku a ba gajiyayyu ba?”
6 Now he said this, not out of concern for the needy, but because he was a thief and, since he held the purse, he used to carry what was put into it.
Ya fadi haka ba don ya damu da gajiyayyu ba, amma domin shi barawo ne: shi ne ma'aji, kuma yana sata daga jakkar kudi.
7 But Jesus said: “Permit her, so that she may keep it against the day of my burial.
Yesu ya ce, “Ku kyale ta ta ajiye abinda ta tanada domin jana'iza ta.
8 For the poor, you have with you always. But me, you do always not have.”
Gajiyayyu suna tare da ku a koyaushe, ni kuwa ba zan kasance da ku koyaushe ba.
9 Now a great multitude of the Jews knew that he was in that place, and so they came, not so much because of Jesus, but so that they might see Lazarus, whom he had raised from the dead.
To babban taron Yahudawa sun ji cewa Yesu yana wurin, sai suka zo, ba don Yesu kawai ba amma domin su ga Li'azaru, wanda Yesu ya tada daga matattu.
10 And the leaders of the priests planned to put Lazarus to death also.
Sai manyan firistoci suka kulla makirci akan yadda za su kashe Li'azaru shima;
11 For many of the Jews, because of him, were going away and were believing in Jesus.
domin saboda shi ne yahudawa dayawa suka je suka bada gaskiya ga Yesu.
12 Then, on the next day, the great crowd that had come to the feast day, when they had heard that Jesus was coming to Jerusalem,
Kashegari, babban taro suka zo idin. Da suka ji cewa Yesu na zuwa Urushalima,
13 took branches of palm trees, and they went ahead to meet him. And they were crying out: “Hosanna! Blessed is he who arrives in the name of the Lord, the king of Israel!”
Sai suka dauki ganyen dabino suka fita gari suka tare shi da kira mai karfi suna cewa, “Hosanna! Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji, Sarkin Isra'ila.
14 And Jesus found a small donkey, and he sat upon it, just as it is written:
Yesu ya sami wani Aholakin jaki, ya hau kansa; kamar yadda aka rubuta,
15 “Do not be afraid, daughter of Zion. Behold, your king arrives, sitting on the colt of a donkey.”
“Kada ki ji tsoro ke 'yar Sihiyona; duba, ga Sarkinki na zuwa, zaune a kan danJaki”.
16 At first, his disciples did not realize these things. But when Jesus was glorified, then they remembered that these things were written about him, and that these things happened to him.
Almajiransa basu fahimci wannan al'amari ba da farko, amma bayan da aka daukaka Yesu, sai suka tuna cewa an rubuta wadannan abubuwa game da shi, kuma sun yi masa wadannan abubuwa.
17 And so the crowd that had been with him, when he called Lazarus from the tomb and raised him from the dead, offered testimony.
Sai taron da ke tare da Yesu a ranar da ya kira Li'azaru daga kabari ya kuma tashe shi daga matattu, suka bada shaida.
18 Because of this, too, the crowd went out to meet him. For they heard that he had accomplished this sign.
Domin wannan ne kuma taron suka zo domin su sadu da shi saboda sun ji cewa ya yi wannan alama.
19 Therefore, the Pharisees said among themselves: “Do you see that we are accomplishing nothing? Behold, the entire world has gone after him.”
Don haka, sai farisawa suka shiga magana a tsakanin su suna cewa “Duba, babu abinda zaku iya yi; kun ga, duniya ta gama bin sa.
20 Now there were certain Gentiles among those who went up so that they might worship on the feast day.
Akwai wadansu Helinawa cikin wadanda suka je sujada a idin.
21 Therefore, these approached Philip, who was from Bethsaida of Galilee, and they petitioned him, saying: “Sir, we want to see Jesus.”
Wadannan suka tafi wurin filibus, mutumin Betsaida da ke Galili, suka ce masa, “Mallam, muna so mu ga Yesu.
22 Philip went and told Andrew. Next, Andrew and Philip told Jesus.
Filibus ya tafi ya fadawa Andrawus; sai Andrawus ya tafi tare da Filibus, suka kuwa gaya wa Yesu.
23 But Jesus answered them by saying: “The hour arrives when the Son of man shall be glorified.
Yesu ya amsa masu ya ce, “sa'a ta zo da za'a daukaka Dan mutum.
24 Amen, amen, I say to you, unless the grain of wheat falls to the ground and dies, it remains alone. But if it dies, it yields much fruit.
Hakika, hakika, Ina ce maku, in ba kwayar alkama ta fadi kasa ba ta mutu, za ta kasance ita kadai; amma idan ta mutu, za ta bada 'ya'ya masu yawa.
25 Whoever loves his life, will lose it. And whoever hates his life in this world, preserves it unto eternal life. (aiōnios g166)
Duk wanda yake son ransa, zai rasa shi; amma wanda ba ya son ransa a duniyan nan za ya kiyaye shi domin rayuwa ta har abada. (aiōnios g166)
26 If anyone serves me, let him follow me. And where I am, there too my minister shall be. If anyone has served me, my Father will honor him.
Idan wani na bauta mani, to bari ya biyo ni; kuma duk inda nike, a can bawana zai kasance kuma. Duk wanda ke bauta mani, Uban zai girmama shi.
27 Now my soul is troubled. And what should I say? Father, save me from this hour? But it is for this reason that I came to this hour.
Yanzu raina na cikin damuwa, to me zan ce? 'Uba, ka cece ni daga wannan sa'a? Amma Saboda wannan dalili ne na zo wannan sa'a.
28 Father, glorify your name!” And then a voice came from heaven, “I have glorified it, and I will glorify it again.”
Uba, ka daukaka sunanka”. Sai wata murya daga sama ta ce, “Na daukaka shi, zan kuma sake daukaka shi.
29 Therefore, the crowd, which was standing near and had heard it, said that it was like thunder. Others were saying, “An Angel was speaking with him.”
Daganan sai taron dake tsaye kuma suka ji muryar, suka ce an yi tsawa. Wasu suka ce, “Mala'ika ya yi magana da shi”.
30 Jesus responded and said: “This voice came, not for my sake, but for your sakes.
Yesu ya amsa ya ce, “wannnan murya ta zo ba saboda ni ba, amma domin ku.”
31 Now is the judgment of the world. Now will the prince of this world be cast out.
Yanzu za'a shar'anta duniya. Yanzu za'a kori mai mulkin duniyan nan.
32 And when I have been lifted up from the earth, I will draw all things to myself.”
Sa, annan ni, idan an daga ni daga duniya, zan jawo dukan mutane zuwa gare ni”.
33 (Now he said this, signifying what kind of death he would die.)
Ya fadi wannan ne domin ya nuna irin mutuwar da za ya yi.
34 The crowd answered him: “We have heard, from the law, that the Christ remains forever. And so how can you say, ‘The Son of man must be lifted up?’ Who is this Son of man?” (aiōn g165)
Taro suka amsa masa cewa, “Mun ji a cikin shari'a cewa Almasihu za ya kasance har abada. Yaya za ka ce, 'za'a daga dan mutum'? Wanene wannan dan mutum?” (aiōn g165)
35 Therefore, Jesus said to them: “For a brief time, the Light is among you. Walk while you have the Light, so that the darkness may not overtake you. But whoever walks in darkness does not know where is he going.
Yesu ya ce masu, “Nan da lokaci kadan za ku kasance da haske, ku yi tafiya tun haske na tare da ku, kada duhu ya mamaye ku. Wanda ke tafiya cikin duhu, bai san inda za shi ba.
36 While you have the Light, believe in the Light, so that you may be sons of the Light.” Jesus spoke these things, and then he went away and hid himself from them.
Ku gaskata ga haske tun yana tare da ku domin ku zama yayan haske”. Yesu ya fadi wadannan abubuwa sannan ya tafi ya boye masu.
37 And although he had done such great signs in their presence, they did not believe in him,
Kodashike Yesu ya yi alamu da dama a gabansu, duk da haka ba su gaskata shi ba.
38 so that the word of the prophet Isaiah might be fulfilled, which says: “Lord, who has believed in our hearing? And to whom has the arm of the Lord been revealed?”
Saboda maganar annabi Ishaya ta cika, wadda ya ce, “Ubangiji, wa ya gaskata rahoton mu? Ga wa kuma hannun Ubangiji ya bayyana?
39 Because of this, they were not able to believe, for Isaiah said again:
Saboda wannan dalili basu gaskata ba, gama Ishaya ya sake cewa,
40 “He has blinded their eyes, and hardened their heart, so that they may not see with their eyes, and understand with their heart, and be converted: and then I would heal them.”
ya makantar da su, ya kuma taurare zuciyarsu, saboda kada su gani da idanunsu, su kuma sami fahimta da zuciyarsu, su juyo wurina in warkar da su.
41 These things Isaiah said, when he saw his glory and was speaking about him.
Ishaya ya fadi wadannan abubuwa ne domin ya hangi daukakar Yesu ya kuma yi magana game da shi.
42 Yet truly, many of the leaders also believed in him. But because of the Pharisees, they did not confess him, so that they would not be cast out of the synagogue.
Amma duk da haka, dayawa cikin shugabanni suka gaskata Yesu. Amma saboda farisawa, basu shaida shi a sarari ba, domin kada a kore su daga majami'a.
43 For they loved the glory of men more than the glory of God.
Suna son yabo daga mutane fiye da yabon dake zuwa daga Allah.
44 But Jesus cried out and said: “Whoever believes in me, does not believe in me, but in him who sent me.
Yesu ya yi magana da babbar murya, ya ce, “Wanda ya gaskata ni, ba ni yake gaskatawa kadai ba, amma kuma yana gaskata wanda ya aiko ni,
45 And whoever sees me, sees him who sent me.
kuma wanda ke gani na, yana ganin shi wanda ya aiko ni.
46 I have arrived as a light to the world, so that all who believe in me might not remain in darkness.
Na zo ne a matsayin haske a duniya, saboda duk wanda ya gaskata da ni ba za ya yi tafiya cikin duhu ba.
47 And if anyone has heard my words and not kept them, I do not judge him. For I did not come so that I may judge the world, but so that I may save the world.
Duk wanda ya ji maganata baya gaskata ba, ba ni hukunta shi; gama ban zo in yi wa duniya hukunci ba, amma don in ceci duniya.
48 Whoever despises me and does not accept my words has one who judges him. The word that I have spoken, the same shall judge him on the last day.
Wanda ya ki ni, ya kuma ki ya karbi magana ta, akwai wanda za ya yi masa hukunci. Kalmar da na fada, ita ce za ta yi masa hukunci a rana ta karshe.
49 For I am not speaking from myself, but from the Father who sent me. He gave a commandment to me as to what I should say and how I should speak.
Maganar da ni ke yi, ba ra'ayina ba ne. Amma Uba wanda ya aiko ni shi ke bani umarni game da abin da zan ce da abin da zan fadi.
50 And I know that his commandment is eternal life. Therefore, the things that I speak, just as the Father has said to me, so also do I speak.” (aiōnios g166)
Na san umarninsa rai ne madawwami, don haka na ce - kamar yadda Uba ya fada, haka ni ma nake fadi.” (aiōnios g166)

< John 12 >