< Job 37 >

1 At this, my heart became frightened, and it has been moved from its place.
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
2 Pay close attention to the alarm of his voice and to the sound that proceeds from his mouth.
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
3 He beholds everything under the heavens, and his light reaches beyond the ends of the earth.
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
4 After this, a noise will sound; he will thunder with the voice of his greatness, and it will not be tracked down, yet his voice will be obeyed.
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
5 God will thunder with his voice miraculously, for he performs great and unsearchable things.
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
6 He commands the snow to descend on earth, and the winter rains, and the shower of his strength.
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
7 He signs the hand of all men, so that each one may know his works.
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
8 The beast will enter his hiding-place, and he will remain in his cave.
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
9 From the interior, a storm will come forth, and a cold winter from the north.
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10 As God breathes out, frost forms, and the waters are poured forth very widely again.
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11 Crops desire clouds, and the clouds scatter their light.
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12 It shines all around, wherever the will of him that governs them will lead, to anywhere he will command, over the whole face of the earth,
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13 whether in one tribe, or in his own region, or in whatever place of his mercy that he will order them to be found.
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
14 Listen to these things, Job. Stand up and consider the wonders of God.
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
15 Do you know when God ordered the rains, so as to show the light of his clouds?
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
16 Do you know the great paths of the clouds, and the perfect sciences?
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
17 Are not your garments hot, when the south wind blows across the land?
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
18 Perhaps you have made the heavens with him, which are very solid, as if they had been cast from brass.
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
19 Reveal to us what we should say to him, for, of course, we are wrapped in darkness.
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
20 Who will explain to him the things that I am saying? Even while a man is still speaking, he will be devoured.
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
21 Although they do not see the light, the air will be thickened suddenly into clouds, and the wind, passing by, will drive them away.
Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
22 Riches arrive from the north, and fearful praise reaches out to God.
Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
23 We are not worthy to be able to find him. Great in strength, great in judgment, great in justice: he is indescribable.
Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
24 Therefore, men will fear him, and all those who seem to themselves to be wise, will not dare to contemplate him.
Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”

< Job 37 >