< Job 36 >

1 Continuing in a similar manner, Eliu had this to say:
Elihu ya ci gaba,
2 Bear with me for a little while and I will show you; for I have still more to say in favor of God.
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 I will review my knowledge from the beginning, and I will prove my Maker to be just.
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 For truly my words are without any falsehood and perfect knowledge will be proven to you.
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 God does not abandon the powerful, for he himself is also powerful.
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 But he does not save the impious, though he grants judgment to the poor.
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 He will not take his eyes away from the just, and he continually establishes kings on their throne, and they are exalted.
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 And, if they are in captivity, or are bound with the chains of poverty,
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 he will reveal to them their works, as well as their sinfulness, in that they were violent.
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 Likewise, he will open their ears to his correction, and he will speak to them, so that they may return from iniquity.
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 If they listen and obey, they will fill their days with goodness and complete their years in glory.
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 But if they will not listen, they will pass away by the sword and will be consumed by foolishness.
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 The false and the crafty provoke the wrath of God, yet they do not cry out to him when they are chained.
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 Their soul will die in a storm, and their life, among the unmanly.
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 He will rescue the poor from his anguish, and he will open his ear during tribulation.
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 Therefore, he will save you from the narrow mouth very widely, even though it has no foundation under it. Moreover, your respite at table will be full of fatness.
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 Your case has been judged like that of the impious; you will withdraw your plea and your judgment.
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 Therefore, do not let anger overwhelm you so that you oppress another; neither should you allow a multitude of gifts to influence you.
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 Lay down your greatness without distress, and put aside all of your power with courage.
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 Do not prolong the night, even if people rise on their behalf.
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 Be careful that you do not turn to iniquity; for, after your misery, you have begun to follow this.
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 Behold, God is exalted in his strength, and there is no one like him among the law-givers.
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 Who is able to investigate his ways? And who can say, “You have done iniquity,” to him?
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 Remember that you are ignorant of his work, yet men have sung its praises.
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 All men consider him; and each one ponders from a distance.
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 Behold, God is great, defeating our knowledge; the number of his years is inestimable.
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 He carries away the drops of rain, and he sends forth showers like a raging whirlpool;
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 they flow from the clouds that are woven above everything.
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 If he wills it, he extends the clouds as his tent
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 and shines with his light from above; likewise, he covers the oceans within his tent.
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 For he judges the people by these things, and he gives food to a multitude of mortals.
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 Within his hands, he hides the light, and he commands it to come forth again.
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 He announces it to his friend, for it is his possession and he is able to reach out to it.
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.

< Job 36 >