< Job 35 >

1 After this, Eliu again spoke in this way:
Sai Elihu ya ce,
2 Does it seem right to you in your thoughts, that you should say, “I am more just than God?”
“Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
3 For you said, “Having done what is right does not please you,” and, “How will it benefit you, if I sin?”
Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
4 And so, I will respond to your words, and to your friends who are with you.
“Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
5 Look up towards heaven and consider; also, think about the sky, which is higher than you.
Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
6 If you sin, how will it hurt him? And if your iniquities are multiplied, what will you do against him?
In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
7 Furthermore, if you act justly, what will you give him, or what will he receive from your hand?
In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
8 Your impiety may hurt a man who is like you, though your justice may help the son of the man.
Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
9 Because of the multitude of false accusers, they will cry out; and they will lament because of the strong arm of the tyrants.
“Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
10 Yet he has not said: “Where is God, who made me, who has given songs in the night,
Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
11 who teaches us in addition to the beasts of the earth, and who educates us along with the birds of the air?”
wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
12 There they will cry, and he will not heed them, because of the arrogance of the wicked.
Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
13 Therefore, God does not hear in vain, and the Almighty will look into each and every case.
Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
14 And so, when you say, “He does not examine,” be judged before him, but wait for him.
Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
15 For, at the present time, he does not bring forth his fury, nor does he punish sin exceedingly.
Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
16 Therefore, Job has opened his mouth in vain and has multiplied words without knowledge.
Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”

< Job 35 >