< Job 28 >

1 Silver has its fissures where it is first found, and gold has a place where it is melted.
Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
2 Iron is taken from the earth, and ore, unbound by heat, is turned into brass.
Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
3 He has established a time for darkness, and he has settled on an end for all things, as well as for the stone that is in the gloom and shadow of death.
Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
4 The burning separates a pilgrim people from those who have been forgotten by the feet of the destitute man and from the unapproachable.
Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
5 The land, where bread appeared in its place, has been destroyed by fire.
Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
6 Its stones are embedded with sapphires, and its soil, with gold.
akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
7 The bird does not know its path, nor has the eye of the vulture beheld it.
Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
8 The sons of merchants have not walked there, nor has the lioness traveled through it.
Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
9 He has stretched out his hand to the rocks; he has overturned the foundations of the mountains.
Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
10 He has cut rivers through the rocks, and his eye has seen all precious things.
Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
11 The depths of rivers he has also examined, and he has brought hidden things into the light.
Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
12 But, in truth, where is wisdom to be found, and where is the place of understanding?
Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
13 Man does not know its price, nor is it found in the land of those who live in sweetness.
Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
14 The abyss declares, “It is not in me.” And the sea says, “It is not with me.”
Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
15 The finest gold will not be paid for it, nor will silver be weighed in exchange for it.
Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
16 It will not be compared with the dyed colors of India, nor with the very costly stone sardonyx, nor with the sapphire.
Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
17 Neither gold nor crystal will be its equal; neither will vessels of gold be fitted for it.
Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
18 The exalted and the eminent will not be remembered in comparison with it. Yet wisdom is drawn out of concealment.
Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
19 The topaz of Ethiopia will not be equal to it, nor will it be compared to the purest dyes.
Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
20 So then, where does wisdom begin, and where is the place of understanding?
“To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
21 It has been hidden from the eyes of all living things, just as the birds of the heavens escape notice.
An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
22 Perdition and death have said, “With our ears, we have heard its fame.”
Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
23 God understands its way, and he knows its location.
Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
24 For he beholds the limits of the world, and he looks upon all things that are under heaven.
Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
25 He created a counterweight for the winds, and he suspended the waters to measure them.
Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
26 At that time, he gave a law to the rain and a path to the resounding storms.
Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
27 Then he saw and explained it, and he made ready and examined it.
sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
28 And he said to man, “Behold the fear of the Lord. Such is wisdom. And to withdraw from evil, this is understanding.”
Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”

< Job 28 >