< Job 26 >

1 Then Job responded by saying:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Whose assistant are you? Is he weak-minded? And do you sustain the arm of him that is not strong?
“Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
3 To whom have you given advice? Perhaps it is to him that has no wisdom or prudence that you have revealed your many ideas.
Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
4 Who is it that you wanted to teach? Was it not him that created the breath of life?
Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
5 Behold, giant things groan under the waters, and they dwell with them.
“Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
6 The underworld is naked before him, and there is no covering for perdition. (Sheol h7585)
Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol h7585)
7 He stretched out the North over emptiness, and he suspended the land over nothing.
Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
8 He secures the waters in his clouds, so that they do not burst forth downward all at once.
Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
9 He holds back the face of his throne, and he stretches his cloud over it.
Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
10 He has set limits around the waters, until light and darkness shall reach their limit.
ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
11 The pillars of heaven tremble and are frightened at his nod.
Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
12 By his strength, the seas suddenly gather together, and his foresight has struck the arrogant.
Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
13 His spirit has adorned the heavens, and his birthing hand has brought forth the winding serpent.
Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
14 Behold, these things have been said about his ways in part, and, since we barely have heard a small drop of his word, who will be able to gaze upon the thunder of his greatness?
Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”

< Job 26 >