< Job 21 >

1 Then Job responded by saying:
Sai Ayuba ya amsa,
2 I beseech you to hear my words and to do penance.
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Permit me, and I will speak, and afterwards, if you see fit, you can laugh at my words.
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 Is my dispute against man, so that I would have no reason to be discouraged?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Listen to me and be astonished, and place a finger over your mouth.
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 As for me, when I think it over, I am afraid, and trembling convulses my body.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 Why then do the impious live, having been lifted up and strengthened with riches?
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 They see their offspring continue before them: a commotion of close relatives and of children’s children in their sight.
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Their houses have been secure and peaceable, and there is no staff of God over them.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 Their cattle have conceived and have not miscarried; their cow has given birth and is not deprived of her newborn.
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 Their little ones go out like a flock, and their children jump around playfully.
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 They take up the timbrel and the lyre, and they rejoice at the sound of the organ.
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 Their days are prolonged in wealth, yet, in an instant, they descend into hell. (Sheol h7585)
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
14 Who has said to God, “Depart from us, for we do not want the knowledge of your ways.
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 Who is the Almighty that we should serve him? And how is it helpful to us if we pray to him?”
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 It is true that their good things are not in their power. May the counsel of the impious be far from me!
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 How often will the lamp of the wicked be extinguished, and a deluge overtake them, and how often will he distribute the afflictions of his wrath?
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 They will be like chaff before the face of the wind, and like ashes that the whirlwind scatters.
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 God will preserve the grief of the father for his sons, and, when he repays, then he will understand.
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 His eyes will see his own destruction, and he will drink from the wrath of the Almighty.
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 For what does he care what happens to his house after him, or if the number of its months are reduced by half?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 Can anyone teach holy knowledge to God, who judges the exalted?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 This one dies strong and healthy, rich and happy.
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 His gut is full of fat and his bones are moistened with marrow.
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 In truth, another dies in bitterness of soul, without any resources.
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 And yet they will sleep together in the dust, and worms will cover them.
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 Surely, I know your thoughts and your sinful judgments against me.
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 For you say, “Where is the house of the ruler, and where are the tabernacles of the impious?”
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 Ask any passerby whom you wish, and you will realize that he understands these same things:
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 that the evil-doer is reserved for the day of destruction, and he will be led to the day of wrath.
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 Who will reprove his way to his face, and who will repay him for what he has done?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 He will be led to the tomb, and he will remain awake in the chaos of the dead.
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 He has been found acceptable to the banks of the River of Lamentation, and he will draw any man towards him, and there are countless before him.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 Therefore, how long will you console me in vain, when your answer is shown to be repugnant to truth?
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”

< Job 21 >