< Job 13 >

1 Behold, my eye has seen all these things, and my ear has heard, and I have understood each one.
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
2 In conformity with your knowledge, I also know. I am not inferior to you.
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
3 Yet I speak this way to the Almighty, and I desire to argue with God,
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
4 having first shown that you fabricate lies and cultivate perverse teachings.
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
5 And I wish that you would remain silent, so that you would be counted among the wise.
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
6 Therefore, listen to my correction, and pay attention to the judgment of my lips.
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7 Does God require your lie, so that you would speak deceitfully for him?
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8 Have you taken his place, and do you struggle to give judgment in favor of God?
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9 Or, will it please him, from whom nothing can be concealed? Or, will he be deceived, like a man, by your deceitfulness?
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10 He will accuse you because in secret you have preempted his presence.
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11 As soon as he moves himself, he will disturb you, and his dread will fall over you.
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12 Your remembrance will be compared to ashes, and your necks will be reduced to clay.
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
13 Be silent for a little while, so that I may speak whatever my mind suggests to me.
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
14 Why do I wound my flesh with my teeth, and carry my soul in my hands?
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
15 And now, if he would kill me, I will hope in him; in this, truly, I will correct my ways in his sight.
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
16 And he will be my savior, for no hypocrite at all will approach in his sight.
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
17 Listen to my words, and perceive an enigma with your ears.
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
18 If I will be judged, I know that I will be found to be just.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
19 Who is it that will go to judgment with me? Let him approach. Why should I be consumed in silence?
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
20 Do not do such things to me twice, and then I will not hide from your face.
“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
21 Take your hand far away from me, and do not let your dread terrify me.
Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
22 Call me, and I will answer you, or else I will speak, and you can answer me.
Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
23 How many iniquities and sins do I have? Reveal my crimes and offenses to me.
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
24 Why do you conceal your face and consider me to be your enemy?
Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
25 Against a leaf, which is carried away by the wind, you reveal your power, and you pursue dry straw.
Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
26 For you write bitter things against me, and you want to consume me for the sins of my youth.
Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
27 You have put my feet on a tether, and you have observed all my paths, and you have considered the steps of my feet.
Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
28 I will be left to decay like something rotten and like a garment that is being eaten by moths.
“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.

< Job 13 >