< Jeremiah 41 >

1 And it happened that, in the seventh month, Ishmael, the son of Nethaniah, the son of Elishama of royal descent, with the nobles of the king, and accompanied by ten men, went to Gedaliah, the son of Ahikam, at Mizpah. And they ate bread together there, in Mizpah.
A wata na goma sha bakwai sai Ishmayel ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake mai jinin sarauta yake kuma ɗaya daga cikin hafsoshin sarki, ya zo tare da mutum goma wurin Gedaliya ɗan Ahikam a Mizfa. Yayinda suke ci tare a can,
2 Then Ishmael, the son of Nethaniah, rose up, and the ten men who were with him, and they struck down Gedaliah, the son of Ahikam, the son of Shaphan, with the sword, and they killed him whom the king of Babylon had made governor over the land.
sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutum goma waɗanda suke tare da shi suka kashe Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da takobi, suka kashe wannan da sarkin Babilon ya naɗa a matsayin gwamna a kan ƙasar.
3 Likewise, Ishmael struck down all the Jews who were with Gedaliah at Mizpah, with the Chaldeans who were found there, and the men of war.
Ishmayel ya kuma kashe dukan Yahudawan da suke tare da Gedaliya a Mizfa, haka ma ya yi da sojojin Babiloniyawan da suke can.
4 Then, on the second day after he had killed Gedaliah, while no one yet knew of it,
Kashegari bayan an kashe Gedaliya, kafin wani ya san abin da ya faru,
5 men arrived from Shechem, and from Shiloh, and from Samaria, eighty men, with their beards shaved, and their garments rent, and unbathed. And they had gifts and frankincense in hand, so that they might make an offering in the house of the Lord.
sai ga mutane tamanin daga Shekem, Shilo da Samariya suka zo da gemunsu a aske, da tufafinsu a kece, da jikunansu a tsage, suka kawo hadayun gari da turare tare da su a gidan Ubangiji.
6 Therefore, Ishmael, the son of Nethaniah, departing from Mizpah to meet them, went forth weeping as he was walking. And when he had met them, he said to them, “Come to Gedaliah, the son of Ahikam.”
Ishmayel ɗan Netaniya ya fito daga Mizfa don yă sadu da su. Sa’ad da ya sadu da su, sai ya ce, “Ku zo wurin Gedaliya ɗan Ahikam.”
7 And when they had arrived at the center of the city, Ishmael, the son of Nethaniah, put them to death around the public cistern, he and the men who were with him.
Da suka shiga cikin birni, sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutanen da suke tare da shi suka karkashe su suka zubar a rijiya.
8 But ten men were found among them, who said to Ishmael: “Do not kill us! For in the field we have storehouses of grain and barley and oil and honey.” And so he ceased, and he did not put them to death with their brothers.
Amma goma daga cikinsu suka ce wa Ishmayel, “Kada ka kashe mu, muna da alkama da sha’ir, mai da kuma zuma, a ɓoye a gona.” Saboda haka ka bar mu kada ka kashe mu tare da sauran.
9 Now the cistern, into which Ishmael cast all the dead bodies of the men whom he had struck down because of Gedaliah, is the same one that king Asa made out of fear of Baasha, the king of Israel. This same cistern Ishmael, the son of Nethaniah, filled with those who were slain.
To, rijiyar da ya zubar da gawawwakin mutanen da ya kashe tare da ta Gedaliya ita ce wadda Sarki Asa ya haƙa a matsayin kāriya saboda Ba’asha sarkin Isra’ila. Ishmayel ɗan Netaniya ya cika ta da gawawwaki.
10 Then Ishmael led away captive all the remnant of the people who were at Mizpah, the king’s daughters as well as all the people who remained at Mizpah, whom Nebuzaradan, the leader of the military, had committed to Gedaliah, the son of Ahikam. And Ishmael, the son of Nethaniah, seized them and went away, so that he might go over to the sons of Ammon.
Ishmayel ya mai da dukan sauran mutanen da suke Mizfa bayi’ya’yan sarki mata tare da dukan sauran da aka bari a can, waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari a hannun Gedaliya ɗan Ahikam. Ishmayel ɗan Netaniya ya kwashe su ganima, ya tashi don yă haye zuwa wurin Ammonawa.
11 But Johanan, the son of Kareah, and all the leaders of the fighters who were with him, heard about all the evil that Ishmael, the son of Nethaniah, had done.
Sa’ad da Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka ji dukan laifofin da Ishmayel ɗan Netaniya ya aikata,
12 And taking all the men, they set out to make war against Ishmael, the son of Nethaniah. And they found him at the great waters that are in Gibeon.
sai suka kwashe dukan mutanensu suka tafi don su yaƙi Ishmayel ɗan Netaniya. Suka iske shi kusa da babban tafki a Gibeyon.
13 And when all the people who were with Ishmael had seen Johanan, the son of Kareah, and all the leaders of the fighters who were with him, they rejoiced.
Sa’ad da dukan mutanen da suke tare da Ishmayel suka ga Yohanan ɗan Kareya da shugabannin sojojin da suke tare da shi, sai suka yi farin ciki.
14 And all the people whom Ishmael had seized turned back to Mizpah. And they returned and went over to Johanan, the son of Kareah.
Dukan mutanen da Ishmayel ya kame a Mizfa suka juya, suka tafi wurin Yohanan ɗan Kareya.
15 But Ishmael, the son of Nethaniah, fled with eight men from the face of Johanan, and they went over to the sons of Ammon.
Amma Ishmayel ɗan Netaniya da mutanensa takwas suka tsere daga Yohanan suka gudu zuwa wurin Ammonawa.
16 Therefore, Johanan, the son of Kareah, and all the leaders of the fighters who were with him, took from Mizpah the entire remnant of the common people, whom they had led away from Ishmael, the son of Nethaniah, after he had struck down Gedaliah, the son of Ahikam. These were strong men of battle, and women, and children, and eunuchs: those whom he had led away from Gibeon.
Sai Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka bi da dukan waɗanda suka tsira daga Mizfa waɗanda ya karɓe daga Ishmayel ɗan Netaniya bayan ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wato, sojoji, mata, yara da fadawan da ya kawo daga Gibeyon
17 And they went away and settled as sojourners at Chimham, which is near Bethlehem, so that they might continue on and enter into Egypt,
Sai suka ci gaba, suka dakata a Gerut Kimham kusa da Betlehem a kan hanyarsu zuwa Masar
18 away from the face of the Chaldeans. For they were afraid of them, because Ishmael, the son of Nethaniah, had struck down Gedaliah, the son of Ahikam, whom the king of Babylon had made governor in the land of Judah.
don su kuɓuce wa Babiloniyawa. Sun ji tsoronsu domin Ishmayel ɗan Netaniya ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wanda sarkin Babilon ya naɗa gwamna a kan ƙasar.

< Jeremiah 41 >