< Jeremiah 37 >

1 And then king Zedekiah, the son of Josiah, reigned in place of Jeconiah, the son of Jehoiakim. For Nebuchadnezzar, the king of Babylon, appointed him as king in the land of Judah.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya naɗa Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda; ya yi mulki a madadin Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim.
2 And neither he himself, nor his servants, nor the people of the land, obeyed the words of the Lord, which he spoke by the hand of Jeremiah, the prophet.
Shi da masu yin masa hidima da mutanen ƙasar ba su kula da maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya annabi ba.
3 And king Zedekiah sent Jehucal, the son of Shelemiah, and Zephaniah, the son of Maaseiah, the priest, to Jeremiah the prophet, saying: “Pray to the Lord our God for us.”
Sai sarki Zedekiya ya aiki Yehukal ɗan Shelemiya tare da firist nan Zefaniya ɗan Ma’asehiya da wannan saƙo cewa, “Ina roƙonka ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnmu saboda mu.”
4 Now Jeremiah was walking freely in the midst of the people. For they had not yet sent him into the custody of the prison.
To, fa, Irmiya ya sami’yancin kai da kawowa a cikin mutane, gama ba a riga an sa shi a kurkuku ba.
5 And then the army of Pharaoh went forth from Egypt. And hearing this, the Chaldeans, who were besieging Jerusalem, withdrew from Jerusalem.
Sojojin Fir’auna suka fita daga Masar, sa’ad da Babiloniyawa waɗanda suke ƙawanya wa Urushalima suka ji labari game da su, sai suka janye daga Urushalima.
6 And the word of the Lord came to Jeremiah the prophet, saying:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya annabi cewa,
7 “Thus says the Lord, the God of Israel: So shall you say to the king of Judah, who sent you to question me: Behold, the army of Pharaoh, which has gone forth in assistance to you, will return to their own land, into Egypt.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aika a neme ni cewa, ‘Sojojin Fir’aunan da suka fito su taimake ka, za su koma ƙasarsu, Masar.
8 And the Chaldeans will return and will make war against this city. And they will seize it and burn it with fire.
Sa’an nan Babiloniyawa za su koma su yaƙi wannan birni su ci ta su kuma ƙone shi.’
9 Thus says the Lord: Do not be willing to deceive your own souls, saying: ‘The Chaldeans will certainly withdraw and go away from us.’ For they will not go away.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku ruɗe kanku, kuna tsammani, ‘Tabbatacce Babiloniyawa sun bar mu.’ Ba za su bari ba!
10 But even if you were to strike down the entire army of the Chaldeans who are fighting against you, and if there were left behind from among them only a few wounded men, they would rise up, each one from his tent, and they would burn this city with fire.”
Ko da a ce za ku ci dukan sojojin Babiloniyawan da suke yaƙi da ku har raunana ne kawai aka bari a tentunansu, za su fito su ƙone wannan birni.”
11 Therefore, when the army of the Chaldeans had withdrawn from Jerusalem because of Pharaoh’s army,
Bayan sojojin Babiloniyawa suka janye daga Urushalima saboda sojojin Fir’auna,
12 Jeremiah went forth from Jerusalem, to go into the land of Benjamin, and to distribute a possession there, in the sight of the citizens.
sai Irmiya ya bar birnin don yă je yankin Benyamin ya sami rabon mallaka a cikin mutane a can.
13 And when he had arrived at the gate of Benjamin, the keeper of the gate, whose turn it was to be there, was named Irijah, the son of Shelemiah, the son of Hananiah. And he apprehended Jeremiah the prophet, saying, “You are fleeing to the Chaldeans.”
Amma sa’ad da ya kai Ƙofar Benyamin, sai hafsa mai tsaro, wanda ake kira Iriya ɗan Shelemiya, ɗan Hananiya, ya kama shi ya kuma ce, “Kana gudu daga Babiloniyawa ne!”
14 And Jeremiah responded: “That is false. I am not fleeing to the Chaldeans.” But he did not listen to him. And so Irijah took Jeremiah, and he brought him to the leaders.
Sai Irmiya ya ce, “Ba gaskiya ba ce, ba na gudu daga Babiloniyawa.” Amma Iriya bai saurare shi ba; a maimako, ya kama Irmiya ya kawo shi wurin fadawa.
15 Therefore, the leaders were angry with Jeremiah, and so they beat him and sent him to the prison that was in the house of Jonathan, the scribe. For he was the chief over the prison.
Suka yi fushi da Irmiya suka sa aka yi masa dūka aka kuma jefa shi cikin kurkuku a gidan Yonatan magatakarda, gama an mai da gidansa ya zama kurkuku.
16 And so Jeremiah went into the house of the prison and into a dungeon. And Jeremiah sat there for many days.
Aka sa Irmiya a can cikin kurkuku, inda ya kasance kwanaki masu yawa.
17 Then Zedekiah the king, sending, took him out and questioned him secretly in his house, and he said: “Do you think that there is any word from the Lord?” And Jeremiah said: “There is.” And he said: “You will be delivered into the hands of the king of Babylon.”
Sa’an nan Sarki Zedekiya ya aika a kawo shi aka kuma kawo shi fada, inda ya tambaye shi a kaɗaice ya ce, “Akwai wata magana daga Ubangiji?” Irmiya ya amsa ya ce, “I, za a ba da kai ga sarkin Babilon.”
18 And Jeremiah said to king Zedekiah: “How have I sinned against you, or your servants, or your people, such that you would cast me into a house of imprisonment?
Sai Irmiya ya ce wa Sarki Zedekiya, “Wane laifi na yi maka ko fadawanka ko kuwa wannan mutane, da ka sa aka jefa ni cikin kurkuku?
19 Where are your prophets, who were prophesying to you, and who were saying: ‘The king of Babylon will not overwhelm you and this land?’
Ina annabawanka waɗanda suka yi maka annabci suna cewa, ‘Sarkin Babilon ba zai yaƙe ka ko wannan ƙasa ba’?
20 Now therefore, listen, I beg you, my lord the king. Let my petition prevail in your sight. And do not send me back into the house of Jonathan the scribe, lest I die there.”
Amma yanzu, ranka yă daɗe, sarkina, ka saurara. Bari in kawo kukata a gabanka. Kada ka mai da ni gidan Yonatan magatakarda, in ba haka zan mutu a can.”
21 Then king Zedekiah instructed that Jeremiah be confined to the vestibule of the prison, and that they should give him a twist of bread daily, along with stew, until all the bread in the city had been consumed. And Jeremiah remained at the entrance of the prison.
Sarki Zedekiya ya yi umarni a ajiye Irmiya a sansanin matsara a kuma ba shi burodi daga titin masu gashin burodi kowace rana sai duka burodi a birnin ya ƙare. Saboda haka Irmiya ya zauna a sansanin matsara.

< Jeremiah 37 >