< Jeremiah 3 >

1 “It is commonly said: ‘If a man has divorced his wife, and she departs from him, she will marry another man.’ So why would he return to her again? Is not that woman polluted and defiled? But you have fornicated yourself with many lovers. Even so, return to me, says the Lord, and I will accept you.
“In mutum ya saki matarsa ta kuwa bar shi ta auri wani mutum, zai iya komo da ita kuma? Ƙasar ba za tă ƙazantu gaba ɗaya ba? Amma kun yi rayuwa kamar karuwa da masoya masu yawa yanzu za ki komo wurina?” In ji Ubangiji.
2 Lift your eyes straight up, and see where you did not debase yourself. You were sitting in the roadways, waiting for them, like a robber in the wilderness. And you have polluted the land by your fornications and by your wickedness.
“Ta da idanu ki duba tsaunuka ki gani. Akwai wani wurin da ba a kwana da ke ba? A gefen hanya kin zauna kina jiran masoyanki, kin zauna kamar makiyayi a hamada. Kin ƙazantar da ƙasar da karuwancinki da muguntarki.
3 For this reason, the rain showers were withheld, and there were no late season rains. You made your face like that of a promiscuous woman; you were not willing to blush.
Saboda haka an hana yayyafi, kuma babu ruwan bazara da ya sauka. Duk da haka kina da irin kallon da karuwa takan yi; kin ƙi ki ji kunya.
4 Therefore, at least from this moment on, call out to me: ‘You are my father, the guide of my virginity.’
Yanzu ba kin kira ni, ‘Mahaifina, abokina daga ƙuruciyata ba,
5 Why should you be angry unceasingly? And will you continue in this to the end? Behold, you have spoken and done evil, for you were able to do so.”
kullum za ka riƙa fushi? Hasalarka za tă ci gaba har abada ne?’ Haka kike magana, amma kina aikata dukan muguntar da kika iya yi.”
6 And, in the days of king Josiah, the Lord said to me: “Have you not seen what the apostate Israel has done? She has brought herself up to every lofty mountain, and she has lain down under every leafy tree, and she has committed fornication there.
A zamanin Sarki Yosiya, Ubangiji ya ce mini, “Ka ga abin da marar amincin nan, Isra’ila ta yi? Ta haura kan kowane tudu mai tsayi da kowane gindin itace mai duhuwa ta yi zina a can.
7 And when she had done all these things, I said: ‘Return to me.’ But she did not return. And her deceitful sister Judah saw this:
Na yi zaton bayan ta yi wannan duka, za tă komo wurina amma ba tă yi haka ba,’yar’uwarta marar aminci nan Yahuda ta gani.
8 that because the apostate Israel had committed adultery, I had dismissed her and had given her a bill of divorce. Yet her deceitful sister Judah was not afraid. But she, too, went and committed fornication herself.
Na ba wa Isra’ila marar bangaskiya takardar saki na kuwa kore ta saboda duk zinanta. Duk da haka na ga cewa’yar’uwarta marar amincin nan Yahuda ba ta da tsoro; ita ma ta fita ta yi zina.
9 And by the act of her fornication, she defiled the land. For she committed adultery with that which is stone and wood.
Domin fasikancin Isra’ila bai yi tasiri gare ta ba, sai ta ƙazantar da ƙasar ta kuma yi zina da dutse da kuma itace.
10 And after all these things, her deceitful sister Judah has not returned to me with her whole heart, but with lies, says the Lord.”
Duk da wannan duka, Yahuda’yar’uwarta rashin amincin ba tă komo gare ni da dukan zuciyarta ba, sai a munafunce,” in ji Ubangiji.
11 And the Lord said to me: “The apostate Israel has justified her own soul by comparing herself to the deceitful Judah.
Ubangiji ya ce mini, “Isra’ila marar bangaskiya ta fi Yahuda marar aminci.
12 Go, and proclaim these words toward the north, and you shall say: Return, O apostate Israel, says the Lord. For I will not avert my face from you. For I am holy, says the Lord, and I will not be angry forever.
Ka tafi, ka yi shelar saƙon nan wajen arewa cewa, “‘Ki komo, Isra’ila marar bangaskiya,’ in ji Ubangiji, ‘Ba zan ƙara yin fushi da ke ba, gama ni mai jinƙai ne,’ in ji Ubangiji, ‘Ba zan yi fushi da ke har abada ba.
13 So then, truly acknowledge your iniquity, that you have betrayed the Lord your God, and that you have spread your ways to strangers, under every leafy tree, and that you have not listened to my voice, says the Lord.
Ki dai yarda da laifinki kin yi wa Ubangiji Allahnki tawaye, kin watsar da alheranki ga baƙin alloli a ƙarƙashin kowane itace mai duhuwa, ba ki kuwa yi mini biyayya ba,’” in ji Ubangiji.
14 Convert, O rebellious sons, says the Lord. For I am your leader. And so, I will take you, one from a city, and two from a family, and I will lead you into Zion.
“Ku komo, ku mutane marasa bangaskiya,” in ji Ubangiji, “gama ni ne mijinku. Zan ɗauke ku, ɗaya daga garuruwanku da kuma biyu daga zuriyarku in kawo ku a Sihiyona.
15 And I will give you pastors according to my own heart. And they will feed you with knowledge and doctrine.
Sa’an nan zan ba ku makiyaya da suke yin abin da zuciyata take so, waɗanda za su bishe ku da sani da kuma fahimi.
16 And when you have been multiplied and increased in the land in those days, says the Lord, they will no longer say: ‘The Ark of the covenant of the Lord!’ And it will not enter into the heart, and they will not call it to mind. It will neither be visited, nor made use of, any longer.
A kwanakin, sa’ad da kuka ƙaru sosai a ƙasar,” in ji Ubangiji, “mutane ba za su ƙara yin magana a kan, ‘Akwatin alkawarin Ubangiji ba.’ Ba zai ƙara shiga zuciyarsu ko su tuna ba; ko su bukace shi, ko kuwa su yi wani irinsa ba.
17 In that time, Jerusalem will be called: ‘The Throne of the Lord.’ And all the nations will be gathered to it, in the name of the Lord, in Jerusalem. And they will not walk after the depravity of their own most wicked heart.
A lokacin za su ce da Urushalima Kursiyin Ubangiji, kuma dukan al’ummai za su taru a Urushalima don su girmama sunan Ubangiji. Ba za su ƙara bin taurinkai zuciyarsu mai mugunta ba.
18 In those days, the house of Judah will go to the house of Israel, and they will come from the land of the north, at the same time, to the land that I gave to your fathers.
A kwanakin gidan Yahuda zai haɗu da gidan Isra’ila, tare kuma za su zo daga ƙasar da take wajen arewa zuwa ƙasar da na ba kakanninsu gādo.
19 But I said: How shall I place you among the sons, and distribute to you a desirable land, the preeminent inheritance of the host of the Gentiles? And I said: You will call me Father, and you will not cease to walk after me.
“Ni kaina na faɗa, “‘Da farin ciki zan ɗauke ki kamar’ya’yana maza in ba ki ƙasa mai daɗi, gādo mafi kyau da wata al’umma.’ Na zaci za ki kira ni ‘Mahaifi’ ba za ki ƙara rabuwa da bina ba.
20 But, in the same way that a woman spurns her lover, so also has the house of Israel spurned me, says the Lord.”
Amma kamar mace marar aminci ga mijinta, haka kika kasance marar aminci gare ni, ya gidan Isra’ila,” in ji Ubangiji.
21 A voice has been heard in the highways, the weeping and wailing of the sons of Israel. For they have made their own ways sinful; they have forgotten the Lord their God.
An ji kuka a filayen tuddai, kuka da roƙon mutanen Isra’ila, domin sun lalace hanyoyinsu sun kuma manta da Ubangiji Allahnsu.
22 “Convert, O rebellious sons! And I will heal your rebelliousness.” “Behold, we are returning to you. For you are the Lord our God!
“Ku komo, mutane marasa bangaskiya; zan warkar da ku daga ja da bayanku.” “I, za mu zo wurinka, gama kai ne Ubangiji Allahnmu.
23 Truly, the hills were liars, with the multitude of the mountains. Truly, the salvation of Israel is in the Lord our God.
Tabbatacce hayaniyar bin gumaka a kan tuddai da duwatsu banza ne; tabbatacce a wurin Ubangiji Allahnmu ne akwai ceton Isra’ila.
24 Confusion has devoured the labor of our fathers, from our youth, with their flocks and their herds, with their sons and their daughters.
Daga ƙuruciyarmu allolin kunya sun cinye mu amfanin wahalar kakanninmu garkunan tumakinsu da na awakinsu, yaransu maza da mata.
25 We will sleep in our confusion, and our disgrace will cover us. For we have sinned against the Lord our God: we and our fathers, from our youth, even to this day. And we have not listened to the voice of the Lord our God.”
Bari mu kwanta mu sha kunya, bari kuma kunyarmu ta rufe mu. Mun yi wa Ubangiji Allahnmu zunubi, da mu da kakanninmu; daga ƙuruciyarmu har yă zuwa yau ba mu yi wa Ubangiji Allahnmu biyayya ba.”

< Jeremiah 3 >