< Jeremiah 29 >

1 And these are the words of the letter which Jeremiah, the prophet, sent from Jerusalem to the remnant of the elders of the transmigration, and to the priests, and to the prophets, and to all the people, whom Nebuchadnezzar had led away from Jerusalem to Babylon,
Ga abin da yake cikin wasiƙar annabi Irmiya da ya aika daga Urushalima zuwa ga sauran dattawan da suka ragu a cikin masu zaman bauta da kuma zuwa ga firistoci, annabawa da kuma dukan sauran mutanen da Nebukadnezzar ya kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
2 after king Jeconiah, with the queen, and the eunuchs, and the leaders of Judah and of Jerusalem, and the craftsmen and engravers, had departed from Jerusalem.
(Wannan ya faru bayan Sarki Yekoniya da mahaifiyar sarauniya, shugabannin fada da kuma dukan shugabannin Yahuda da Urushalima, gwanayen sana’a da masu sassaƙa suka tafi zaman bauta daga Urushalima.)
3 It was sent by the hand of Elasah, the son of Shaphan, and by Gemariah, the son of Hilkiah, whom Zedekiah, the king of Judah, sent to Babylon to Nebuchadnezzar, the king of Babylon, saying:
Ya ba da wasiƙar ta hannun Eleyasa ɗan Shafan da Gemariya ɗan Hilkiya, waɗanda Zedekiya sarkin Yahuda ya aika wurin Sarki Nebukadnezzar a Babilon. Wasiƙar ta ce,
4 “Thus says the Lord of hosts, the God of Israel, to all who have been taken away, whom I have caused to be transferred from Jerusalem to Babylon:
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ga dukan waɗanda aka kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
5 Build houses and live in them. And plant gardens, and eat from their fruit.
“Ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.
6 Take wives, and conceive sons and daughters. And give wives to your sons, and give your daughters to husbands, and let them bear sons and daughters. And be multiplied there, and do not choose to be few in number.
Ku yi aure ku kuma haifi’ya’ya maza da mata; ku nemi mata wa’ya’yanku maza, ku kuma ba da’ya’yanku mata ga aure, saboda su ma za su haifi’ya’ya maza da mata. Ku riɓaɓɓanya a can, kada ku ragu.
7 And seek the peace of the city, to which I have caused you to be taken away, and pray to the Lord on its behalf. For your peace will be in its peace.
Haka kuma, ku nemi zaman salama da cin gaba a birnin da aka kai ku zaman bauta. Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda birnin, domin in ya ci gaba, ku ma za ku ci gaba.”
8 For thus says the Lord of hosts, the God of Israel: Do not allow your prophets and your diviners, who are in your midst, to seduce you. And you should pay no attention to your dreams, which you are dreaming.
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Kada ku bar annabawa da masu sihiri a cikinku su ruɗe ku. Kada ku saurari mafarkan da dā kuke ƙarfafa su su yi.
9 For they prophesy falsely to you in my name, and I have not sent them, says the Lord.
Suna muku annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba,” in ji Ubangiji.
10 For thus says the Lord: When the seventy years will begin to be completed in Babylon, I will visit you. And I will raise up over you my good word, so that I may lead you back to this place.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sa’ad da shekaru saba’in suka cika a Babilon, zan zo muku in cika alkawarin alherina don in komo da ku zuwa wannan wuri.
11 For I know the thoughts that I think over you, says the Lord: thoughts of peace and not of affliction, so that I may give you patience and an end.
Gama na san shirye-shiryen da na yi muku,” in ji Ubangiji, “shirye-shiryen cin gaba ba na cutarwa ba, shirye-shiryen ba ku sa zuciya da kuma na nan gaba.
12 And you shall call upon me, and you shall go forth. And you shall pray to me, and I will heed you.
Sa’an nan za ku kira gare ni ku zo ku kuma yi addu’a gare ni, zan kuwa ji ku.
13 You shall seek me. And you will find me, when you have sought me with your whole heart.
Za ku neme ni ku kuwa same ni sa’ad da kuka neme ni da dukan zuciyarku.
14 And I will be found by you, says the Lord. And I will lead you back from your captivity. And I will gather you from all the nations and all the places, to which I have expelled you, says the Lord. And I will return you from the place to which I sent you into captivity.
Za ku same ni,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku daga bauta. Zan tattaro ku daga dukan al’ummai in sa ku inda na kore ku,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku zuwa wurin da na kwashe ku zuwa zaman bauta.”
15 For you have said: ‘The Lord has raised up prophets for us in Babylon.’
Za ku iya ce, “Ubangiji ya tā da annabawa saboda mu a Babilon.”
16 For thus says the Lord, to the king who sits upon the throne of David, and to all the people who live in this city, to your brothers who have not departed with you in the transmigration:
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarki, wanda yake zaune a kursiyin Dawuda da kuma dukan mutanen da suka ragu a wannan birni,’yan’uwanku waɗanda ba su tafi tare da ku zuwa zaman bauta ba.
17 Thus says the Lord of hosts: Behold, I will send among them the sword, and famine, and pestilence. And I will make them like the bad figs, which cannot be eaten, because they are very bad.
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu zan kuma sa su zama kamar ɓaure marar amfani da suka yi munin da ba a iya ci.
18 And I will pursue them with the sword, and with famine, and with pestilence. And I will give them over to affliction, amid all the kingdoms of the earth: as a curse, and in stupor, and with hissing, and as a disgrace among all the nations to which I have driven them out.
Zan fafare su da takobi, yunwa da annoba zan kuma sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya da kuma abin la’ana da abin bantsoro, abin dariya da abin reni, a cikin dukan al’umman da aka kore su zuwa.
19 For they have not listened to my words, says the Lord, which I sent to them through my servants, the prophets, rising while it was still night, and sending. But you have not listened, says the Lord.
Gama ba su saurari maganata ba,” in ji Ubangiji, “maganar da na aika gare su sau da sau ta bayina annabawa. Ku kuma masu zaman bauta ba ku saurara ba,” in ji Ubangiji.
20 Therefore, listen to the word of the Lord, all you of the transmigration, whom I have sent away from Jerusalem into Babylon.
Saboda haka, ku ji maganar Ubangiji, dukanku masu zaman bauta waɗanda na aika daga Urushalima zuwa Babilon.
21 Thus says the Lord of hosts, the God of Israel, to Ahab, the son of Kolaiah, and to Zedekiah, the son of Maaseiah, who prophesy falsely to you in my name: Behold, I will deliver them into the hands of Nebuchadnezzar, the king of Babylon, and he will strike them down before your eyes.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa game da Ahab ɗan Kolahiya da Zedekiya ɗan Ma’asehiya, waɗanda suke muku annabcin ƙarya da sunana. “Zan ba da su ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai kuwa kashe su a gaban idanunku.
22 And a curse will be taken up about them, by all the captives of Judah that are in Babylon, saying: ‘May the Lord make you like Zedekiah, and like Ahab, whom the king of Babylon fried in the fire!’
Saboda su, dukan masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suke a Babilon za su yi amfani da wannan la’ana cewa, ‘Ubangiji ka yi da mu kamar Zedekiya da Ahab waɗanda sarkin Babilon ya ƙone da wuta.’
23 For they have acted foolishly in Israel, and they have committed adultery with the wives of their friends, and they have spoken lying words in my name, which I did not command them. I am the Judge and the Witness, says the Lord.
Gama sun aikata munanan abubuwa a Isra’ila; sun yi zina da matan maƙwabtansu kuma da sunana suka yi ƙarya, waɗanda ban faɗa musu su yi ba. Na san wannan kuma ni shaida ne ga haka,” in ji Ubangiji.
24 And to Shemaiah of Nehelam, you shall say:
Faɗa wa Shemahiya mutumin Nehelam,
25 Thus says the Lord of hosts, the God of Israel: Similarly, you have sent letters in your name to all the people that are in Jerusalem, and to Zephaniah, the son of Maaseiah, the priest, and to all the priests, saying:
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka aika da wasiƙu da sunanka ga dukan mutane a Urushalima, zuwa ga Zefaniya ɗan Ma’asehiya firist da kuma ga sauran firistoci. Ka ce wa Zefaniya,
26 ‘The Lord has made you priest in place of Jehoiada, the priest, so that you would be the ruler in the house of the Lord over every man who raves and prophesies, to send him to the stocks and to prison.
‘Ubangiji ya naɗa ka firist a wurin Yehohiyada don ka lura da gidan Ubangiji; ya kamata ka sa kowane mahaukaci wanda yake yi kamar annabi cikin turu da kuma a kangi.
27 And now why have you not rebuked Jeremiah of Anathoth, who prophesies to you?
To, me ya sa ba ka tsawata wa Irmiya daga Anatot, wanda yana ɗauka kansa annabi a cikinku ba?
28 For about this, he has sent to us in Babylon, saying: It is a long time. Build houses and live in them. And plant gardens, and eat from their fruits.’”
Ya aiko mana da saƙonsa a Babilon cewa zai ɗauki lokaci ƙwarai. Saboda haka ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.’”
29 Thus, Zephaniah, the priest, read this letter, in the hearing of Jeremiah the prophet.
Zefaniya firist kuwa, ya karanta wasiƙar annabi Irmiya.
30 And the word of the Lord came to Jeremiah, saying:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
31 “Send to all those of the transmigration, saying: Thus says the Lord to Shemaiah of Nehelam: Because Shemaiah has prophesied to you, though I did not send him, and because he has caused you to trust in a lie:
“Ka aika da wannan saƙo zuwa ga dukan masu zaman bauta cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shemahiya, mutumin Nehelam. Domin Shemahiya ya yi muku annabci, ko da yake ban aike shi ba, ya kuma sa kuka gaskata ƙarya,
32 For this reason, thus says the Lord: Behold, I will visit upon Shemaiah of Nehelam, and upon his offspring. There will not be, for him, even one man sitting in the midst of this people. And he will not see the good that I will accomplish for my people, says the Lord. For he has spoken a betrayal against the Lord.”
ga abin da Ubangiji yana cewa, tabbatacce zan hukunta Shemahiya mutumin Nehelam da zuriyarsa. Ba zai kasance da wani da ya rage a cikin wannan mutane ba, ba kuwa zai ga abubuwa alherin da zan yi wa mutanena ba, in ji Ubangiji, domin ya yi wa’azin tawaye a kaina.’”

< Jeremiah 29 >