< Jeremiah 16 >

1 And the word of the Lord came to me, saying:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “You shall not take a wife, and there shall be no sons or daughters for you in this place.
“Kada ka yi aure ka haifi’ya’ya maza da mata a wannan wuri.”
3 For thus says the Lord concerning the sons and daughters who are conceived in this place, and concerning their mothers who give birth to them, and concerning their fathers, from whose stock they have been born in this land:
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da’ya’ya maza da matan da aka haifa a wannan ƙasa da kuma game da matan da suke iyayensu da suke mazan da iyayensu.
4 They will die from grievous mortal illnesses. They will not be mourned, and they will not be buried. They will be like manure on the face of the earth. And they will be consumed by sword and by famine. And their dead bodies will be food for the birds of the air and the beasts of the land.”
“Za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi kuka dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba, amma za a bar su a juji. Takobi da yunwa ne za su hallaka su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji na duniya.”
5 For thus says the Lord: “You shall not enter the house of feasting, and you shall not go to mourn or to console them. For I have taken away from this people, says the Lord, my peace, my mercy, and my pity.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ka shiga gidan da akwai abincin makoki; kada ka tafi ka yi makoki ko ka nuna juyayi, domin na janye albarkata, ƙaunata da tausayina daga wannan mutane,” in ji Ubangiji.
6 Both the great and the small will die in this land. They will not be buried, and they will not be mourned. And no one will cut themselves or make themselves bald on their behalf.
“Manya da ƙanana duka za su mutu a wannan ƙasa. Ba za a binne su ba, ba kuwa za a yi makokinsu ba, kuma ba wanda zai tsaga kansa ko ya aske kansa saboda su.
7 And they will not break bread among themselves for the sake of him who mourns, so as to console him over the dead. And they will not give them a chalice to drink, so as to console them over their father and mother.
Ba wanda zai ba da abinci don yă ta’azantar da waɗanda suke makoki saboda matattu, kai, ko saboda mahaifi ko mahaifiya ma ba kuwa wani da zai ba da abin sha don yă ta’azantar da su.
8 And so, you shall not enter the house of feasting, so as to sit with them, and to eat and drink.”
“Kada kuma ka shiga gidan da ake biki ka zauna don ci da sha.
9 For thus says the Lord of hosts, the God of Israel: “Behold, I will take away from this place, in your sight and in your days, the voice of gladness and the voice of rejoicing, the voice of the groom and the voice of the bride.
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa a idanunka da kuma a kwanakinka zan kawo ƙarshen muryar farin ciki da murna da kuma muryoyin amarya da ango a wannan wuri.
10 And when you announce all these words to this people, they will say to you: ‘Why would the Lord pronounce all this great evil against us? What is our iniquity and what is our sin that we have committed against the Lord our God?’
“Sa’ad da ka faɗa wa waɗannan mutane wannan duka suka kuma tambaye ka, ‘Me ya sa Ubangiji ya ƙaddara irin wannan babban masifa a kanmu? Wace mugunta muka yi? Wane zunubi muka aikata wa Ubangiji Allahnmu?’
11 And you shall say to them: It is because your fathers abandoned me, says the Lord. And they went after strange gods, and they served them and adored them. And they abandoned me, and they did not keep my law.
Sai ka ce musu, ‘Wannan ya zama haka domin kakanninku sun rabu da ni,’ in ji Ubangiji, ‘suka bi waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Suka rabu da ni, ba su kuwa kiyaye dokata ba.
12 But you have acted even worse than your fathers. For behold, each one walks after the depravity of his own evil heart, so that he does not listen to me.
Amma kun yi laifi fiye da kakanninku. Duba yadda kowannenku yana bin taurin muguwar zuciyarsa a maimakon yin mini biyayya.
13 And so, I will cast you out of this land, into a land that you do not know, and that your fathers did not know. And in that place, you will serve, day and night, strange gods who will not give you rest.
Saboda haka zan fitar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasar da ku da kakanninku ba ku taɓa sani ba, a can kuwa za ku bauta wa waɗansu alloli dare da rana, gama ba zan nuna muku tagomashi ba.’
14 Therefore, behold, the days are approaching, says the Lord, when it will no longer be said, ‘As the Lord lives, who led the sons of Israel away from the land of Egypt,’
“Amma fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “da mutane ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga Masar,’
15 but instead, ‘As the Lord lives, who led the sons of Israel away from the land of the north,’ and from all the lands to which I have cast them out. And I will lead them back into their own land, which I gave to their fathers.
amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashe da ya kora su.’ Gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba wa kakanninsu.
16 Behold, I will send many fishermen, says the Lord, and they will fish for them. And after this, I will send many hunters to them, and they will hunt for them on every mountain, and on every hilltop, and in the caverns of the rocks.
“Amma yanzu zan aiko a kira masunta masu yawa su zo,” in ji Ubangiji, “za su kuma kama su. Bayan wannan zan aiko a kira mafarauta su zo, su farauce su daga kowane dutse da tudu da kuma daga kogwannin duwatsu.
17 For my eyes are upon all their ways. They have not been hidden from my face, and their iniquity has not been concealed from my eyes.
Idanuna suna a kan dukan hanyoyinsu; ba a ɓoye suke daga gare ni, kuma zunubansu ba a ɓoye suke a idanuna ba.
18 But first, I will repay their double iniquities and their sins. For they have defiled my land with the dead bodies of their idols, and they have filled my inheritance with their abominations.”
Zan riɓaɓɓanya sakayyar da zan yi musu saboda muguntarsu da zunubinsu, domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun gumakansu marasa rai, suka kuma cika abin gādona da gumakansu na banƙyama.”
19 “O Lord, my strength, and my health, and my refuge in the day of tribulation: the Gentiles will approach you from the ends of the earth, and they will say: ‘Truly, our fathers possessed a lie, an emptiness that has not benefited them.’
Ya Ubangiji, ƙarfina da katangana, mafakata a lokacin damuwa, gare ka al’ummai za su zo daga iyakokin duniya su ce, “Kakanninmu ba su mallaki kome ba sai allolin ƙarya, gumakan banza da ba su yi musu amfani ba.
20 How can man make gods for himself, though these are not gods?”
Mutane kan yi allolinsu ne? I, amma waɗannan ba alloli ba ne!”
21 “Concerning this, behold: I will make it clear to them, in this turn. I will reveal to them my hand and my virtue. And they will know that the Lord is my name.”
“Saboda haka zan koya musu a wannan lokaci zan koya musu ikona da ƙarfina. Sa’an nan za su sani cewa sunana Ubangiji ne.

< Jeremiah 16 >