< Jeremiah 13 >

1 Thus says the Lord to me: “Go, and obtain for yourself a linen waistcloth. And you shall place it over your loins, and you shall not put it into water.”
Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Tafi ka sayo abin ɗamara na lilin ka sha ɗamara da shi, amma kada ka bari yă taɓa ruwa.”
2 And so I obtained a waistcloth, according to the word of the Lord, and I placed it around my loins.
Saboda haka na sayo abin ɗamara, yadda Ubangiji ya umarce ni, na kuwa sha ɗamara da shi.
3 And the word of the Lord came to me a second time, saying:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini sau na biyu cewa,
4 “Take the waistcloth, which you obtained, which is around your loins, and, rising up, go to the Euphrates, and hide it there in an opening of the rock.”
“Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi yanzu zuwa Fera ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.”
5 And so I went, and I hid it by the Euphrates, just as the Lord had instructed me.
Saboda haka na tafi na ɓoye shi a Fera, yadda Ubangiji ya ce mini.
6 And it happened that, after many days, the Lord said to me: “Rise up, go to the Euphrates, and take from there the waistcloth, which I instructed you to hide there.”
Bayan’yan kwanaki sai Ubangiji ya ce mini, “Tafi yanzu zuwa Fera ka ɗauko abin ɗamara da na ce maka ka ɓoye a can.”
7 And so I went to the Euphrates, and I dug up and took the waistcloth from the place where I had hidden it. And behold, the waistcloth had rotted, so that it was not fit for any use.
Sai na tafi Fera da haka na ɗauko abin ɗamara daga wurin da na ɓoye shi, amma abin ɗamara yanzu ya lalace ya zama ba shi da amfani sam.
8 And the word of the Lord came to me, saying:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
9 “Thus says the Lord: In the same way, I will cause the arrogance of Judah and the arrogance of Jerusalem to rot.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Haka zan lalatar da alfarmar Yahuda da yawan alfarmar Urushalima.
10 This most wicked people, they are not willing to listen to my words, for they walk in the depravity of their own heart, and they have gone after strange gods, so as to serve them and to adore them. And so, they will become like this waistcloth, which is not fit for any use.
Waɗannan mugayen mutane, waɗanda suka ƙi saurari maganata, waɗanda suka biye wa taurin zuciyarsu suka bi waɗansu alloli don su bauta su kuma yi musu sujada, za su zama kamar wannan abin ɗamara gaba ɗaya marasa amfani!
11 For just as the waistcloth clings to the loins of a man, so have I brought close to me the entire house of Israel and the entire house of Judah, says the Lord, so that they would be to me: a people, and a name, and a praise, and a glory. But they did not listen.
Gama kamar yadda abin ɗamara kan kame gindin mutum tam, haka zan daure dukan gidan Isra’ila da dukan gidan Yahuda gare ni,’ in ji Ubangiji, ‘domin su zama jama’a, da suna, da yabo, da daraja a gare ni, amma sun ƙi ji.’
12 Therefore, you shall speak to them this word: Thus says the Lord, the God of Israel: ‘Every bottle will be filled with wine.’ And they will say to you: ‘Are we ignorant that every bottle will be filled with wine?’
“Faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi.’ In kuwa suka ce maka, ‘Ba mu san cewa ya kamata a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi ba?’
13 And you shall say to them: Thus says the Lord: Behold, I will fill all the inhabitants of this land, and the kings from the stock of David who sit upon his throne, and the priests, and the prophets, and all the inhabitants of Jerusalem, unto inebriation.
Sai ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan cika dukan waɗanda suke zama a ƙasar da buguwa, har ma da sarakunan da suke zama a kursiyin Dawuda, firistoci, annabawa da dukan waɗanda suke zaune a Urushalima.
14 And I will scatter them, a man from his brother, and fathers and sons similarly, says the Lord. I will not spare them, and I will not pardon them, and I will not take pity, so as not to destroy them.”
Zan fyaɗe su a kan juna, iyaye da’ya’yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi ko jinƙai, ko juyayi ba zai hana ni hallaka su ba.’”
15 Hear and pay close attention. Do not choose to lift yourself up, for the Lord has spoken.
Ku ji ku kuma saurara, kada ku yi girman kai, gama Ubangiji ya yi magana.
16 Give glory to the Lord your God, before darkness falls, and before your feet stumble on the darkened mountains. You will expect light, but he will turn it into the shadow of death and into utter darkness.
Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnku kafin ya kawo duhu, kafin ƙafafunku su yi tuntuɓe a kan tuddai masu duhu. Za ku sa zuciya ganin haske amma zai mai da shi duhu mai kauri ya kuma canja shi zuwa duhu baƙi ƙirin.
17 But if you will not listen to this, then my soul will weep in secret before the face of your pride. It will weep bitterly, and my eyes will flow with tears, because the flock of the Lord has been taken captive.
Amma in ba ku saurara ba, zan yi kuka a ɓoye saboda girmankanku; idanuna za su yi kuka mai zafi, suna zub da hawaye ƙwarai, domin zan kwashe garken Ubangiji zuwa zaman bauta.
18 “Say to the king and to the female ruler: Humble yourselves, sit down. For the crown of your glory has gone down from your head.
Ka faɗa wa sarki da kuma mahaifiyar sarauniya cewa, “Ku sauko daga kursiyinku, gama rawaninku na ɗaukaka za su fāɗi daga kawunanku.”
19 The cities of the south have been closed, and there is no one who may open them. All of Judah has been taken away into complete captivity.
Za a kulle biranen da suke a Negeb, kuma babu wanda zai buɗe su. Za a kwashe dukan Yahuda zuwa zaman bauta, za a kwashe su tas.
20 Lift up your eyes and see, you who are arriving from the north. Where is the flock that was given to you, your famous cattle?
Ku tā da idanunku ku ga waɗanda suke zuwa daga arewa. Ina garken da aka ba ku tumakin da kuke taƙama a kai?
21 What will you say when he visits upon you? For you have taught them against you, and you have instructed them with your own head. Will not pains take hold of you, as with a woman in labor?
Me za ku ce sa’ad da Ubangiji ya naɗa muku waɗanda ku kanku kuka koya musu a matsayi abokai na musamman? Ashe, azaba ba za tă auko muku kamar na mace mai naƙuda ba?
22 But if you say in your heart, ‘Why have these things happened to me?’ it is because of the greatness of your iniquity that your shame has been uncovered and the soles of your feet have been defiled.
In kuma kuka tambaye kanku “Me ya sa wannan ya faru da mu?” Wannan kuwa saboda yawan zunubanku ne ya sa fatarinku ya yage aka kuma wahalshe jikinku.
23 If the Ethiopian is able to change his skin, or the leopard is able to change his spots, then you also may be able to do well, though you have learned evil.
Mutumin Habasha zai iya canja launin fatar jikinsa ko damisa ta canja dabbare dabbarenta? Ba za ku iya yin alheri ku da kuka saba da yin mugunta ba.
24 And I will scatter them like chaff, which is carried away by the wind in the desert.
“Zan watsar da ku kamar yayin da iskar hamada take hurawa.
25 This is your lot, and this is the portion of your measure from me, says the Lord, because you have forgotten me, and you have had confidence in what is false.
Rabonku ne wannan, sashen da na auka muku,” in ji Ubangiji “domin kun manta da ni kuka kuma dogara ga allolin ƙarya.
26 Therefore, I have even bared your thighs before your face, and your shame has been seen.
Zan kware fatarinku sama ya rufe fuskarku don a iya ga tsiraicinku
27 For I have seen your adulteries, and your neighing for the wickedness of your fornication, and your abominations upon the hills in the field. Woe to you, Jerusalem! How much longer before you will be made clean after me?”
zinace zinacenku da haniniya kamar dawakai, karuwancinku na bankunya! Na ga ayyukanku na banƙyama a kan tuddai da kuma a filaye. Kaitonki, ya Urushalima! Har yaushe za ki ci gaba da rashin tsarki?”

< Jeremiah 13 >