< Isaiah 7 >

1 And it happened in the days of Ahaz, the son of Jotham, the son of Uzziah, the king of Judah, that Rezin, the king of Syria, and Pekah, the son of Remaliah, king of Israel, ascended to Jerusalem to battle against it. But they were not able to defeat it.
Sa’ad da Ahaz ɗan Yotam, ɗan Uzziya, yake sarkin Yahuda, Sarki Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su yaƙi Urushalima, amma ba su iya cinta da yaƙi ba.
2 And they reported to the house of David, saying: “Syria has withdrawn to Ephraim.” And his heart was shaken, with the heart of his people, just as the trees of the forest are moved by the face of the wind.
Sai fa aka faɗa wa gidan Dawuda cewa, “Aram ya haɗa kansa da Efraim”; saboda haka zuciyar Ahaz da ta mutanensa suka firgita, sai ka ce itatuwa a kurmin da iska ta girgiza.
3 And the Lord said to Isaiah: Go out to meet Ahaz, you and your son, Jashub, who was left behind, to the end of the aqueduct, at the upper pool, on the road to the fuller’s field.
Sai Ubangiji ya ce wa Ishaya, “Fita, kai da ɗanka Sheyar-Yashub, don ku sadu da Ahaz a ƙarshen wuriyar da take kawo ruwa daga Tafkin Tudu, a hanyar Filin Mai Wanki.
4 And you shall say to him: “See to it that you are silent. Do not be afraid. And have no dread in your heart over the two tails of these firebrands, nearly extinguished, which are the wrath of the fury of Rezin, king of Syria, and of the son of Remaliah.”
Ka faɗa masa, ‘Ka yi hankali, ka natsu kada kuma ka ji tsoro ko ka damu, kada ka ji tsoron fushin sarki Rezin da na Aram da na ɗan Remaliya, ba wani abu mai hatsari ba ne, bai fi hayaƙin’yan ƙirare biyu da suke cin wuta ba.
5 For Syria has undertaken a plan against you, with the evil of Ephraim and the son of Remaliah, saying:
Aram, Efraim da ɗan Remaliya sun ƙulla maƙarƙashiya, suna cewa,
6 “Let us ascend to Judah, and stir it up, and tear it away for ourselves, and appoint the son of Tabeel as a king in its midst.”
“Bari mu kai wa Yahuda hari; bari mu yayyage su mu rarraba su a tsakaninmu, mu naɗa Tabeyel sarki a kansu.”
7 Thus says the Lord God: This shall not stand, and this shall not be.
Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “‘Ba zai faru ba, ba zai auku ba,
8 For the head of Syria is Damascus, and the head of Damascus is Rezin; and within sixty-five years from now, Ephraim will cease to be a people.
gama kan Aram shi ne Damaskus, kan Damaskus kuma kawai shi ne Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar za a wargaje Efraim har ba za tă iya rayuwa ta zama al’umma ba.
9 For the head of Ephraim is Samaria, and the head of Samaria is the son of Remaliah. If you will not believe, you will not continue.
Kan Efraim shi ne Samariya, kan Samariya kuma kawai shi ne ɗan Remaliya. In ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiyarku ba, ba za ku dawwama ba.’”
10 And the Lord spoke further to Ahaz, saying:
Ubangiji ya kuma yi magana wa Ahaz ya ce,
11 Ask for a sign for yourself from the Lord your God, from the depths below, even to the heights above. (Sheol h7585)
“Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.” (Sheol h7585)
12 And Ahaz said, “I will not ask, for I will not tempt the Lord.”
Amma Ahaz ya ce, “Ba zan nema ba; ba zan gwada Ubangiji ba.”
13 And he said: “Then listen, O house of David. Is it such a small thing for you to trouble men, that you must also trouble my God?
Sa’an nan Ishaya ya ce, “To, ku saurara, ya ku gidan Dawuda! Abin kirki kuke yi ne da kuka ƙure haƙurin jama’a? Ko haƙurin Allah ne kuma kuke so ku ƙure?
14 For this reason, the Lord himself will grant to you a sign. Behold, a virgin will conceive, and she will give birth to a son, and his name will be called Immanuel.
Saboda haka Ubangiji kansa zai ba ku alama. Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, za tă kuwa kira shi Immanuwel.
15 He will eat butter and honey, so that he may know to reject evil and to choose good.
In ya yi girma har ya isa yanke shawara don kansa, madara da zuma ne abincinsa.
16 But even before the boy knows to refuse evil and to choose good, the land that you detest will be abandoned by the face of her two kings.
Amma kafin yaron yă isa yanke shawara yă ƙi abin da yake mummuna, yă zaɓi abin da yake nagari, ƙasashen sarakunan nan biyu da kuke tsoro za su zama kango.
17 The Lord will lead over you, and over your people, and over the house of your father, such days as have not occurred since the days of the separation of Ephraim from Judah by the king of the Assyrians.
Ubangiji zai aukar maka da kwanakin wahala, kai da jama’arka, da dukan iyalin gidan sarauta, waɗanda suka fi muni tun lokacin da aka raba mulkin Efraim daga na Yahuda, zai kawo sarkin Assuriya.”
18 And this shall be in that day: the Lord will call for the fly, which is in the most distant parts of the rivers of Egypt, and for the swarm, which is in the land of Assur.
A wannan rana Ubangiji zai yi feɗuwa yă kira ƙudaje daga rafuffuka masu nisa na Masar da kuma ƙudan zuma daga ƙasar Assuriya.
19 And they will arrive, and they all will rest in the torrents of the valleys, and in the caverns of the rocks, and in every thicket, and in every opening.
Za su zo su mamaye kwazazzabai da kogwanni cikin duwatsu, a kan dukan ƙayayyuwa da dukan rammukan ruwa.
20 In that day, the Lord will shave with a razor the ones hired by those who are across the river, by the king of the Assyrians, from the head to the hairs of the feet, with the entire beard.
A wannan rana Ubangiji zai yi amfani da rezan da aka yi haya daga ƙetaren Kogi, sarkin Assuriya ke nan, yă aske kanku da gashin ƙafafunku, zai kuma aske gemunku.
21 And this shall be in that day: a man will raise a cow among oxen, and two sheep,
A ranar, mutum zai bar karsana ɗaya da awaki biyu da rai.
22 and, instead of an abundance of milk, he will eat butter. For all who are left behind in the midst of the land will eat butter and honey.
Kuma saboda yalwa madarar da suke bayarwa, zai kasance da madarar da zai sha. Dukan waɗanda suka rage a ƙasar za su sha madara da zuma.
23 And this shall be in that day: every place, where there were a thousand grapevines worth a thousand pieces of silver, will become thorns and briers.
A wannan rana, a kowane wuri inda akwai kuringa dubu da kuɗinsu ya kai shekel dubu na azurfa, ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne kawai za su kasance a can.
24 They will enter such places with arrows and bows. For briers and thorns will be throughout the entire land.
Mutane za su je can da baka da kibiyoyi, gama ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne za su rufe ƙasar.
25 But as for all the mountains, which will be dug with a hoe, the terror of thorns and briers will not approach those places. And there will be pasture land for oxen, and a range for cattle.”
Game da dukan tuddai da dā ake nome da garemani kuwa, ba za ku ƙara je wurin ba saboda tsoron ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya; za su zama wuraren da ake kai shanu a sake su su yi ta yawo da kansu, tumaki kuma su yi ta gudu.

< Isaiah 7 >