< Isaiah 63 >

1 Who is this, who arrives from Edom with dyed garments from Bozrah? This is the Handsome One in his robe, advancing by the fullness of his strength. It is I, the Speaker of Justice, and I am the Fighter for Salvation.
Wane ne wannan mai zuwa daga Edom, daga Bozra, saye da jajjayen rigunarsa? Wane ne wannan, sanye cikin daraja, tafe cikin girmar ƙarfinsa? “Ni ne, mai magana cikin adalci, mai ikon ceto.”
2 So then, why is your garment red, and why are your vestments like the ones of those who tread the winepress?
Me ya sa rigunanka suka yi ja, sai ka ce na wanda yake tattaka’ya’yan inabi?
3 I have trod the winepress alone. And among the nations, there is no man beside me. I have trampled on them in my fury, and I have tread them down in my wrath. And so, their blood has been sprinkled on my vestments, and I have stained all my garments.
“Na tattake’ya’yan inabi ni kaɗai; cikin al’ummai kuma babu wani tare da ni. Na tattake su cikin fushina Na matse su cikin hasalata; jininsu ya fantsamar wa rigunana, na kuma ɓata dukan tufafina.
4 For the day of vengeance is in my heart. The year of my redemption has arrived.
Gama ranar ɗaukan fansa tana a cikin zuciyata, kuma shekarar fansata ta zo.
5 I gazed around, and there was no one to assist. I sought, and there was no one who would help. And so, my own arm has saved for me, and my own wrath itself has assisted me.
Na duba, amma babu wanda zai taimaka, na yi mamaki cewa ba wanda ya goyi baya; saboda haka hannuna ya yi mini ceto, fushina kuma ya rayar da ni.
6 And I have trampled the peoples in my fury, and I have inebriated them with my indignation, and I have torn down their strength to the ground.
Na tattake al’ummai cikin fushina; cikin hasalata kuma na sa sun bugu na kuma zub da jininsu a ƙasa.”
7 I will remember the compassion of the Lord, the praise of the Lord over all that the Lord has bestowed on us, and over the multitude of his good things for the house of Israel, which he has granted to them according to his leniency, and according to the multitude of his mercies.
Zan ba da labarin alherin Ubangiji, ayyukan da suka sa a yabe shi, bisa ga dukan abubuwan da Ubangiji ya yi mana, I, ayyuka masu kyan da ya yi domin gidan Isra’ila, bisa ga jinƙansa da yawan alheransa.
8 And he said: “Yet truly, these are my people, sons who have not been disowned.” And he became their Savior.
Ya ce, “Babu shakka su mutanena ne,’ya’ya maza waɗanda ba za su ruɗe ni ba”; ta haka ya zama Mai Cetonsu.
9 Throughout all their tribulation, he was not troubled, for the Angel of his presence saved them. With his love, and by his leniency, he has redeemed them, and he has carried them and lifted them up, throughout all the days of the ages.
Cikin dukan damuwarsu shi ma ya damu, mala’ikan da yake gabansa ya cece su. Cikin ƙauna da jinƙai ya fanshe su; ya kuma ɗaga su ya riƙe su dukan kwanakin dā
10 But they themselves provoked to wrath and afflicted his Holy Spirit, and he was turned to be for them like an enemy, and he himself went to war against them.
Duk da haka suka yi tawaye suka ɓata wa Ruhu Mai Tsarki rai. Saboda haka ya juya ya kuma zama abokin gābansu shi kansa kuma ya yaƙe su.
11 And he remembered the days of ancient times, the days of Moses and his people. Where is he who led them out of the sea, with the shepherds of his flock? Where is he who placed his Holy Spirit in their midst?
Sa’an nan mutanensa suka tuna kwanakin dā, kwanakin Musa da mutanensa, ina yake shi wanda ya fitar da su ta teku, da makiyayan garkensa? Ina shi yake wanda ya sa Ruhunsa Mai Tsarki a cikinsu,
12 He led Moses by the right hand, with the arm of his majesty. He split the waters before them, in order to make an everlasting name for himself.
wanda ya aika hannu ɗaukakarsa mai iko ya kasance a hannun dama na Musa, wanda ya raba ruwaye a gabansu, don yă sami wa kansa madawwamin suna,
13 He led them through the abyss, like a horse which does not stumble, in the desert.
wanda ya bishe su cikin zurfafa? Kamar doki a fili, ba su yi tuntuɓe ba;
14 Like an animal who descends to an open field, the Spirit of the Lord was their guide. Thus did you lead your people, in order to make a glorious name for yourself.
kamar shanun da suke gangarawa zuwa kwari, haka Ruhun Ubangiji ya ba su hutu. Ga yadda ka bishe mutanenka don ka ba wa kanka suna mai ɗaukaka.
15 Gaze down from heaven, and behold from your holy habitation and from your glory. Where is your zeal, and your strength, the fullness of your heart and of your compassion? They have held themselves back from me.
Ka duba daga sama ka gani daga kursiyinka da yake bisa, mai tsarki da kuma mai ɗaukaka. Ina kishinka da kuma ikonka? Ka janye juyayi da kuma tausayin da kake yi mana daga gare mu.
16 For you are our Father, and Abraham has not known us, and Israel has been ignorant of us. You are our Father, O Lord our Redeemer. Your name is beyond all ages.
Amma kai Ubanmu ne, ko Ibrahim bai san mu ba Isra’ila kuma bai yarda da mu ba; kai, ya Ubangiji, kai ne Ubanmu, Mai Fansarmu tun fil azal ne sunanka.
17 Why have you allowed us to stray from your ways, O Lord? Why have you hardened our heart, so that we do not fear you? Return, for the sake of your servants, the tribes of your inheritance.
Don me, ya Ubangiji, ka sa muna barin hanyoyinka muka kuma taurare zukatanmu don kada mu girmama ka? Ka komo domin darajar bayinka, kabilan da suke abin gādonka.
18 They have possessed your holy people as if it were nothing. Our enemies have trampled your sanctuary.
Gama a ɗan lokaci mutanenka suka mallaki wurinka mai tsarki, amma yanzu abokan gābanmu sun tattake wurinka mai tsarki.
19 We have become as we were in the beginning, when you did not rule over us, and when we were not called by your name.
Mu naka tun fil azal; ba ka taɓa yin mulki a kansu ba, ba a taɓa kira su da sunanka ba.

< Isaiah 63 >