< Isaiah 56 >

1 Thus says the Lord: Preserve judgment, and accomplish justice. For my salvation is close to its arrival, and my justice is close to being revealed.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku riƙe gaskiya ku yi abin da yake daidai, gama cetona yana kusa za a kuma bayyana adalcina nan da nan.
2 Blessed is the man who does this, and the son of man who holds to this, keeping the Sabbath and not profaning it, guarding his hands and not doing any evil.
Mai albarka ne mutumin da ya aikata wannan, mutumin da ya riƙe kam yana kiyaye Asabbaci ba tare da ƙazantar da shi ba, yana kuma kiyaye kansa daga yin mugun abu.”
3 And let not the son of the new arrival, who adheres to the Lord, speak, saying, “The Lord will divide and separate me from his people.” And let not the eunuch say, “Behold, I am a dry tree.”
Kada baƙon da ya miƙa kansa ga Ubangiji ya ce, “Ai Ubangiji zai ware ni daga mutanensa.” Kada kuma wani bābā ya yi gunaguni cewa, “Ni busasshen itace ne kawai.”
4 For thus says the Lord to the eunuchs: They will keep my Sabbaths, and they will choose the things that I will, and they will hold to my covenant.
Gama ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Wa bābānnin da suna kiyaye Asabbatai, waɗanda suka zaɓi yin abin da ya gamshe ni suna kuma riƙe da alkawarina kankan,
5 I will give them a place in my house, within my walls, and a name better than sons and daughters. I will give them an everlasting name, which will never perish.
a gare su cikin haikalina da kuma bangayensa zan ba da matuni da kuma suna mafi kyau fiye da’ya’ya maza da kuma’ya’ya mata; zan ba su madawwamin sunan da ba za a raba su da shi ba.
6 And the sons of the new arrival, who adhere to the Lord so as to worship him and to love his name, shall be his servants: all who keep the Sabbath without profaning it, and who hold to my covenant.
Baƙin da suka miƙa kansu ga Ubangiji don su bauta masa, su kuma ƙaunaci sunan Ubangiji, waɗanda kuma suke yin masa sujada, duk waɗanda suka kiyaye Asabbaci ba tare da ƙazantar da shi ba suka kuma riƙe alkawarina kankan,
7 I will lead them to my holy mountain, and I will gladden them in my house of prayer. Their holocausts and their victims will be pleasing to me upon my altar. For my house will be called the house of prayer for all peoples.
waɗannan ne zan kai tsattsarkan dutsena in sa su yi farin ciki a gidana na addu’a. Hadayunsu na ƙonawa da sadakokinsu za su zama abin karɓa a bagadena; gama za a ce da gidana gidan addu’a domin dukan al’ummai.”
8 The Lord God, who gathers the dispersed of Israel, says: Even now, I will gather his congregation to him.
Ubangiji Mai Iko Duka ya furta cewa, zai tattara korarru na Isra’ila, “Zan ƙara tattaro waɗansu bayan waɗanda na riga na tattara.”
9 All beasts of the field, all the beasts of the forest: approach and devour!
Ku zo, dukanku namun jeji, ku zo ku ci, dukanku namun jeji!
10 His watchmen are all blind. They are all ignorant. They are mute dogs without the ability to bark, seeing empty things, sleeping and loving dreams.
Matsaran Isra’ila makafi ne, dukansu jahilai ne; dukansu bebayen karnuka ne ba za su iya haushi ba; suna kwance ne kawai suna mafarki, suna son barci ba dama.
11 And these very imprudent dogs have never known satisfaction. The shepherds themselves do not know understanding. All have turned aside in their own way, each one to his own avarice, from the highest even to the least:
Su karnuka ne masu kwaɗayi; ba su taɓa ƙoshi. Su makiyaya ne marasa ganewa; duk sun nufi inda suka ga dama, kowa yana nemar wa kansa riba.
12 “Come, let us take wine, and be filled by inebriation. And as it is today, so shall it be tomorrow and for a long time.”
Kowanne yakan ce, “Zo, bari in samo ruwan inabi! Bari mu cika cikinmu da barasa! Gobe ma zai zama kamar yau, ko ma fiye da haka.”

< Isaiah 56 >