< Isaiah 52 >

1 Rise up, Rise up! Clothe yourself in strength, O Zion! Put on the garments of your glory, O Jerusalem, the city of the Holy One! For the uncircumcised and the unclean will no longer pass through you.
Ki farka, ki farka, ya Sihiyona, ki sanya wa kanki ƙarfi. Ki sa rigarki na daraja, Ya Urushalima, birni mai tsarki. Marasa kaciya da maƙazanta ba za su shi cikinki ba.
2 Shake yourself from the dust! Arise and sit up, O Jerusalem! Loose the chains from your neck, O captive daughter of Zion!
Ki kakkaɓe ƙurarki; ki tashi, ki zauna a kursiyinki, ya Urushalima. Ki’yantar da kanki daga sarƙoƙi a wuyanki, Ke kamammiyar Diyar Sihiyona.
3 For thus says the Lord: You were sold for nothing, and you will be redeemed without money.
Gama ga abin Ubangiji yana cewa, “An sayar da ke ba da kuɗi ba, kuma ba da kuɗi za a fanshe ki ba.”
4 For thus says the Lord God: My people descended into Egypt, in the beginning, in order to sojourn there. But the Assyrian oppressed them, without any cause at all.
Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Da farko mutanena suka gangara zuwa Masar don su zauna; a baya-bayan nan, Assuriya sun zalunce su.
5 And now, what is left for me here, says the Lord? For my people have been taken away without cause. Their lords treat them unjustly, says the Lord. And my name is being continually blasphemed all day long.
“Yanzu kuma me nake da shi a nan?” In ji Ubangiji. “Gama an kwashe mutanena ba a bakin kome ba kuma waɗanda suka mallake su sun yi musu ba’a, Kullum ana cin gaba da yin wa sunana saɓo.
6 Because of this, my people will know my name, in that day. For it is I myself who is speaking. Behold, I am here.
Saboda haka mutanena za su san sunana; saboda haka a wannan rana za su san cewa ni ne wanda ya faɗa wannan. I, ni ne.”
7 How beautiful upon the mountains are the feet of the messenger and the preacher of peace! Announcing good and preaching peace, they are saying to Zion, “Your God will reign!”
Me ya fi wannan kyau a kan duwatsu a ga ƙafafu na masu kawo labari mai daɗi waɗanda suke shelar salama, waɗanda suke kawo labari mai daɗi, waɗanda suke shelar ceto, waɗanda suke ce wa Sihiyona, “Allahnki yana mulki!”
8 It is the voice of your watchmen. They have lifted up their voice. They will praise together. For they will see eye to eye, when the Lord converts Zion.
Ki kasa kunne! Masu tsaronki sun tā da muryoyinsu; tare sun yi sowa ta farin ciki. Sa’ad da Ubangiji ya komo Sihiyona, za su gan shi da idanunsu.
9 Be glad and rejoice together, O deserts of Jerusalem! For the Lord has consoled his people. He has redeemed Jerusalem.
Ku ɓarke cikin waƙoƙin farin ciki gaba ɗaya, kangonki na Urushalima, gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa, ya fanshi Urushalima.
10 The Lord has prepared his holy arm, in the sight of all the Gentiles. And all the ends of the earth will see the salvation of our God.
Ubangiji zai nuna hannunsa mai tsarki a fili a idanun dukan al’ummai, da kuma dukan iyakokin duniya za su gani ceton Allahnmu.
11 Depart, depart, get out of here! Do not be willing to touch what is polluted. Go out from her midst! Be cleansed, you who bear the vessels of the Lord.
Ku fita, ku fita daga can! Kada ku taɓa wani abu marar tsarki! Ku fita daga cikinta ku zama da tsarki, ku da kuke ɗaukan kayan aikin Ubangiji.
12 For you will not go out in a tumult, nor will you take flight in a hurry. For the Lord will precede you, and the God of Israel will gather you.
Amma ba za ku fita a gaggauce ba ko ku tafi da gudu; gama Ubangiji zai ja gabanku, Allah na Isra’ila zai kasance mai tsaron bayanku.
13 Behold, my servant will understand; he will be exalted and lifted up, and he will be very sublime.
Duba, bawana zai aikata abubuwa da hikima; za a tā da shi a kuma ɗaga shi da ɗaukaka ƙwarai.
14 Just as they were stupefied over you, so will his countenance be without glory among men, and his appearance, among the sons of men.
Kamar dai yadda aka kasance da mutane masu yawa waɗanda suka giggice sa’ad da suka gan shi, kamanninsa ya lalace ƙwarai fiye da na kowane mutum siffarsa kuma ta yi muni fiye da yadda ta mutum take,
15 He will sprinkle many nations; kings will close their mouth because of him. And those to whom he was not described, have seen. And those who have not heard, have considered.
haka zai ba al’ummai masu yawa mamaki, sarakuna kuma za su riƙe bakunansu don mamaki. Gama abin da ba a faɗa musu ba, shi za su gani, kuma abin da ba su ji ba, shi za su fahimta.

< Isaiah 52 >