< Isaiah 50 >

1 Thus says the Lord: What is this bill of divorce for your mother, by which I have dismissed her? Or who is my creditor, to whom I have sold you? Behold, you were sold by your iniquities, and I have dismissed your mother for your wickedness.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ina takardar shaida na saki mahaifiyarka daga aure wadda na kora? Ko kuwa ga wanda mutumin da nake bin bashi ne na sayar da kai? Saboda zunubanka aka sayar da kai; saboda laifofinka ne ya sa aka kori mahaifiyarka.
2 For I arrived, and there was no man. I called out, and there was no one who would hear. Has my hand been shortened and become small, so that I am unable to redeem? Or is there no power in me to deliver? Behold, at my rebuke, I will make the sea into a desert. I will turn rivers into dry land. The fish will rot for lack of water and will die of thirst.
Sa’ad da na zo, me ya sa babu kowa? Sa’ad da na yi kira, me ya sa babu wani da ya amsa? Hannuna ya kāsa ne sosai don fansarka? Na rasa ƙarfin kuɓutar da kai ne? Ta wurin tsawatawa kawai na busar da teku, na mai da koguna hamada; kifayensu duk sun ruɓe saboda rashin ruwa suka kuma mutu saboda ƙishi.
3 I will clothe the heavens in darkness, and I will make sackcloth their covering.
Na suturar da sararin sama da duhu na kuma mai da tsummoki abin rufuwarsa.”
4 The Lord has given me a learned tongue, so that I would know how to uphold with a word, one who has weakened. He rises in the morning, he rises to my ear in the morning, so that I may heed him like a teacher.
Ubangiji Mai Iko Duka ya ba ni harshen umarni, don in san maganar da za tă ƙarfafa gajiyayye. Ya farkar da ni da safe, ya farkar da kunnena don in saurara kamar wanda ake koya masa.
5 The Lord God has opened my ear. And I do not contradict him. I have not turned back.
Ubangiji Mai Iko Duka ya buɗe kunnuwana, kuma ban yi tayarwa ba; ban ja da baya ba.
6 I have given my body to those who strike me, and my cheeks to those who plucked them. I have not averted my face from those who rebuked me and who spit on me.
Na ba da bayana ga masu dūkana, kumatuna ga masu jan gemuna; ban ɓoye fuskata daga masu ba’a da masu tofa mini miyau ba.
7 The Lord God is my helper. Therefore, I have not been confounded. Therefore, I have set my face like a very hard rock, and I know that I will not be confounded.
Gama Ubangiji Mai Iko Duka zai taimake ni, ba zan sha kunya ba. Saboda haka na kafa fuskata kamar dutsen ƙanƙara, na kuma sani ba zan sha kunya ba.
8 He who justifies me is near. Who will speak against me? Let us stand together. Who is my adversary? Let him approach me.
Gama shi da zai tabbatar da ni, marar laifi ne yana kusa. Wane ne zai kawo ƙararraki game da ni? Bari mu je ɗakin shari’a tare! Wane ne mai zargina? Bari yă kalubalance ni!
9 Behold, the Lord God is my helper. Who is the one who would condemn me? Behold, they will all be worn away like a garment; the moth will devour them.
Ubangiji Mai Iko Duka ne zai taimake ni. Wane ne zai iya tabbatar da ni mai laifi? Duk za su koɗe kamar riga; asu za su cinye su.
10 Who is there among you who fears the Lord? Who hears the voice of his servant? Who has walked in darkness, and there is no light in him? Let him hope in the name of the Lord, and let him lean upon his God.
Wane ne a cikinku yake tsoron Ubangiji yana kuma yin biyayya ga maganar bawansa? Bari wanda yake tafiya cikin duhu, wanda ba shi da haske, ya dogara a sunan Ubangiji ya kuma dogara ga Allahnsa.
11 Behold, all you who kindle a fire, wrapped in flames: walk in the light of your fire and in the flames that you have kindled. This has been done to you by my hand. You will sleep in anguish.
Amma yanzu fa, dukanku waɗanda kuke ƙuna wuta kuna kuma tanada wa kanku fitilu masu ci, ku je ku yi tafiya a cikin hasken wutarku da na fitilun da kuka ƙuna. Abin da za ku karɓa ke nan daga hannuna. Za ku kwanta a cikin azaba.

< Isaiah 50 >