< Isaiah 45 >

1 Thus says the Lord to my anointed Cyrus, whose right hand I hold, so that I may subjugate the nations before his face, and I may turn the backs of kings, and I may open the doors before him, and so that the gates will not be shut.
“Ga abin da Ubangiji ya faɗa wa shafaffensa, ga Sairus, wanda hannun damansa yana riƙe da shi don yă ci al’ummai a gabansa ya kuma tuɓe makaman sarakuna, don yă buɗe ƙofofi a gabansa don kada a kulle ƙofofi.
2 I will go before you. And I will humble the glorious ones of the earth. I will shatter the gates of brass, and I will break apart the bars of iron.
Zan sha gabanka in baje duwatsu; zan farfashe ƙofofin tagulla in kuma kakkarye ƙyamaren ƙarfe.
3 And I will give you hidden treasures and the knowledge of secret things, so that you may know that I am the Lord, the God of Israel, who calls your name.
Zan ba ka dukiyar duhu, arzikin da aka ajiye a asirtattun wurare, saboda ka san cewa ni ne Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya kira ka da suna.
4 For the sake of Jacob, my servant, and Israel, my elect, I have even called you by your name. I have taken you up, and you have not known me.
Saboda sunan Yaƙub bawana, Isra’ila zaɓaɓɓena, na kira ka da suna na ba ka matsayin bangirma, ko da yake ba ka san ni ba.
5 I am the Lord, and there is no one else. There is no god beside me. I girded you, and you have not known me.
Ni ne Ubangiji, kuma babu wani; in ban da ni babu wani Allah. Zan ƙarfafa ka, ko da yake ba ka san ni ba,
6 So may those who are from the rising of the sun, and those who are from its setting, know that there is no one beside me. I am the Lord, and there is no other.
saboda daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta mutane za su san cewa babu wani in ban da ni. Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
7 I form the light and create the darkness. I make peace and create disaster. I, the Lord, do all these things.
Ni ne na siffanta haske na kuma halicci duhu, ni ne nake ba da nasara in kuma jawo bala’i; ni, Ubangiji ne ke aikata dukan waɗannan abubuwa.
8 Send down dew from above, O heavens, and let the clouds rain down upon the just! Let the earth open and spring forth a savior! And let justice rise up at once! I, the Lord, have created him.
“Ku sammai, ku sauko da adalci kamar ruwan sama; bari gizagizai su zubar da yayyafi kamar adalci. Bari ƙasa ta buɗe, bari ceto ya tsiro, bari adalci ya yi girma tare da shi; ni, Ubangijine, na sa ya faru.
9 Woe to him who contradicts his Maker, a mere shard from an earthen vessel! Should the clay say to the potter, “What are you making?” or, “Your work is not made by your hands?”
“Kaitonka mai gardama da Wanda ya yi ka, da wanda yake kasko a cikin kasko a ƙasa. Yumɓu ya iya ce wa magini, ‘Me kake yi?’ Aikinka na iya cewa, ‘Ba shi da hannuwa’?
10 Woe to him who says to his father, “Why did you conceive?” or to a woman, “Why did you give birth?”
Kaiton wanda yake cewa mahaifinsa, ‘Me ka manta?’ Ko kuwa ga mahaifiyarsa, ‘Me kin haifa?’
11 Thus says the Lord, the Holy One of Israel, his Maker: Would you question me about the future, concerning my sons, and command me concerning the work of my hands?
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, da kuma Mahaliccinsa. Game da abubuwan da ke zuwa, kun tambaye ni game da’ya’yana, ko kuwa kun ba ni umarni game da aikin hannuwana?
12 I made the earth, and I created man upon it. My hand stretched out the heavens, and I have commanded all their hosts.
Ai, ni ne wanda ya yi duniya na kuma halicci mutum a kanta. Hannuwana ne sun miƙe sammai; na umarci rundunar sararin sama.
13 I have raised him up unto justice, and I will direct all his ways. He himself will build my city and release my captives, but not for ransom or gifts, says the Lord, the God of hosts.
Zan tā da Sairus cikin adalcina. Zan sa dukan hanyoyinsa su miƙe. Zai sāke gina birnina ya kuma’yantar da mutanena masu bautar talala, amma ba don wata haya ko lada ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
14 Thus says the Lord: The labor of Egypt, and the business dealings of Ethiopia, and of the Sabeans, men of stature, will pass to you and will be yours. They will walk behind you. They will travel, bound in irons. And they will adore you and petition you: “In you alone is God, and there is no God apart from you.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kayayyakin Masar da hajar Kush, da waɗannan dogayen Sabenawa, za su ƙetaro zuwa wurinku za su kuma zama naku; za su bi bayanku, suna zuwa cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku su roƙe ku, suna cewa, ‘Tabbas Allah yana tare da ku, babu kuma wani; babu wani allah.’”
15 Truly, you are a hidden God, the God of Israel, the Savior.”
Tabbatacce kai ne Allah wanda ya ɓoye kanka, Ya Allah da Mai Ceton Isra’ila.
16 They have all been confounded and should be ashamed! These fabricators of errors have departed together into confusion!
Dukan masu yin gumaka za su sha kunya; za su fita da kunya gaba ɗaya.
17 Israel is saved in the Lord by an eternal salvation. You will not be confounded, and you will not be ashamed, even forever and ever.
Amma Ubangiji zai ceci Isra’ila da madawwamin ceto; ba za ku sāke shan kunya ko ƙasƙanci ba, har abada.
18 For thus says the Lord, who created the heavens, God himself who formed the earth and made it, the very Molder of it. He did not create it to no purpose. He formed it so that it would be inhabited. I am the Lord, and there is no other.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci sammai, shi ne Allah; shi da ya sarrafa ya kuma yi duniya, ya kafa ta; bai halicce ta don ta zama ba kome ba, amma ya yi ta don a zauna a ciki, ya ce, “Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
19 I have not spoken in secret, in a dark place of the earth. I have not said to the offspring of Jacob, “Seek me in vain.” I am the Lord, who speaks justice, who announces what is right.
Ban yi magana asirce ba, daga wani wuri a ƙasar duhu ba; ban faɗa wa zuriyar Yaƙub, ‘Ku neme ni a banza ba.’ Ni, Ubangiji maganar gaskiya nake yi; na furta abin da yake daidai.
20 Assemble yourselves, and approach, and draw near together, you who have been saved among the Gentiles. They lack knowledge, who lift up the wood of their sculpture, and who petition a god unable to save.
“Ku tattaru ku zo; ku taru, ku masu gudun hijira daga al’ummai. Masu jahilci ne waɗanda suke ɗaukan gumakan katakai suna yawo, waɗanda suke addu’a ga allolin da ba za su cece su ba.
21 Announce it, and approach, and consult together. Who has caused this to be heard from the beginning, and who has foretold it from that time? Is it not I, the Lord? And is there some other god beside me? I am a just God who saves, and there is no one except me.
Furta abin da zai kasance, ku gabatar da shi, bari su yi shawara tare. Wa ya faɗa wannan tuntuni, wa ya yi shelar sa a kwanakin dā? Ba ni ba ne, Ubangiji? Kuma babu Allah in ban da ni, Allah mai adalci da kuma Mai Ceto; babu wani sai ni.
22 All ends of the earth, be converted to me, and you will be saved. For I am God, and there is no other.
“Ku juyo gare ni ku sami ceto, dukanku iyakokin duniya; gama ni ne Allah, kuma babu wani.
23 I have sworn by myself. The Word of justice will proceed from my mouth, and it will not turn back. For every knee shall bend to me, and every tongue shall swear it.
Da kaina na rantse, bakina ya furta cikin dukan mutunci kalmar da ba za a janye ba. A gabana kowace gwiwa za tă durƙusa; ta wurina kowane harshe zai rantse.
24 Therefore, he will say, “In the Lord are my justices and my dominion.” They will go to him. And all who fight against him will be confounded.
Za su yi zance game da ni su ce, ‘A cikin Ubangiji kaɗai akwai adalci da kuma ƙarfafawa.’” Duk wanda ya yi fushi da shi zai zo wurinsa ya kuma sha kunya.
25 In the Lord, all the offspring of Israel will be justified and praised.
Amma a cikin Ubangiji dukan zuriyar Isra’ila za su sami adalci za su kuwa yi yabo.

< Isaiah 45 >