< Isaiah 41 >

1 Let the islands be silent before me, and let the nations take new strength. Let them draw near, and then speak. Let us apply for judgment together.
“Ku yi shiru a gabana, ku tsibirai! Bari al’ummai su sabunta ƙarfinsu! Bari su zo gaba su yi magana; bari mu sadu a wurin shari’a.
2 Who has raised up a just man from the east, and has called him to follow him? He will place the nations under his gaze, and he will rule over kings. He will cause them to be like dust before his sword, like chaff driven by the wind before his bow.
“Wa ya zuga wannan daga gabas, yana kiransa cikin adalci ga yin hidima? Ya miƙa masa al’ummai ya kuma yi nasara da sarakuna a gabansa. Ya mai da su ƙura da takobinsa, zuwa inda iska ke hurawa ta wurin bugun da ya yi musu.
3 He will pursue them. He will pass by in peace. No trace will appear after his feet.
Ya fafare su ya kuma yi tafiyarsa lafiya ƙalau, a hanyar da ƙafafunsa ba su taɓa bi ba.
4 Who has worked and accomplished these things, calling to the generations from the beginning? “It is I, the Lord! I am the first and the last.”
Wane ne ya taɓa yin haka ya kuma sa ya faru, yana kira ga tsararraki daga farko? Ni, Ubangiji ina can tun farkonsu ni kuma ina can har ƙarshe, Ni ne shi.”
5 The islands saw it and were afraid. The ends of the earth were stupefied. They drew near and arrived.
Tsibirai sun gan shi suka kuma ji tsoro; iyakokin duniya sun yi rawar jiki. Suka kusato suka kuma zo gaba;
6 Each one will help his neighbor and will say to his brother, “Be strengthened.”
kowa na taimakon wani yana ce wa ɗan’uwansa, “Ka ƙarfafa!”
7 The coppersmith striking with the mallet encouraged him who was forging at that time, saying, “It is ready for soldering.” And he strengthened it with nails, so that it would not be moved.
Masassaƙi yakan ƙarfafa maƙerin zinariya, kuma shi mai gyara da guduma ya yi sumul yakan ƙarfafa mai harhaɗawa. Ya ce game da haɗin, “Ya yi kyau.” Yakan buga ƙusoshi su riƙe gunkin don kada yă fāɗi.
8 But you, O Israel, are my servant, O Jacob, whom I have chosen, the offspring of my friend Abraham.
“Amma kai, ya Isra’ila, bawana, Yaƙub, wanda na zaɓa, zuriyar Ibrahim abokina,
9 For his sake, I have taken you from the ends of the earth, and I have called you from its distant places. And I said to you: “You are my servant. I have chosen you, and I have not cast you aside.”
na ɗauke ka daga iyakar duniya, daga kusurwoyi masu nesa na kira ka. Na ce, ‘Kai bawana ne’; na zaɓe ka ban kuwa ƙi ka ba.
10 Do not be afraid, for I am with you. Do not turn away, for I am your God. I have strengthened you, and I have assisted you, and the right hand of my just one has upheld you.
Saboda haka kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai; kada ka karai, gama ni ne Allahnka. Zan ƙarfafa ka in kuma taimake ka; zan riƙe ka da hannun damana mai adalci.
11 Behold, all who fight against you shall be confounded and ashamed. They will be as if they did not exist, and the men who contradict you will perish.
“Duk wanda ya yi fushi da kai tabbatacce zai sha kunya da ƙasƙanci; waɗanda suka yi hamayya da kai za su zama kamar ba kome ba su kuma hallaka.
12 You will seek them, and you will not find them. The men who rebel against you will be as if they did not exist. And the men who make war against you will be like something that has been consumed.
Ko ka nemi abokan gābanka, ba za ka same su ba. Waɗanda suke yaƙi da kai za su zama kamar ba kome ba.
13 For I am the Lord your God. I take you by your hand, and I say to you: Do not be afraid. I have helped you.
Gama ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya riƙe ka da hannun damana ya kuma ce maka, Kada ka ji tsoro; zan taimake ka.
14 Fear not, O worm of Jacob, you who are dead within Israel. I have helped you, says the Lord, your Redeemer, the Holy One of Israel.
Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub marar ƙarfi, ya ƙaramin Isra’ila, gama ni kaina zan taimake ka,” in ji Ubangiji, Mai Fansarka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
15 I have established you like a new threshing cart, having serrated blades. You will thresh the mountains and crush them. And you will turn the hills into chaff.
“Duba, zan sa ka cikin abin sussuka, saboda kuma mai kaifi mai haƙora da yawa. Za ka yi sussukar duwatsu ka ragargaza su, ka kuma farfashe tuddai su zama kamar yayi.
16 You will winnow them, and the wind will blow them away, and the whirlwind will scatter them. And you shall exult in the Lord; you shall rejoice in the Holy One of Israel.
Za ka tankaɗe su, iska kuma ta kwashe su, guguwa kuma za tă warwatsa su. Amma za ka yi farin ciki a cikin Ubangiji ka kuma ɗaukaka a cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
17 The indigent and the poor are seeking water, but there is none. Their tongue has been dried up by thirst. I, the Lord, will heed them. I, the God of Israel, will not abandon them.
“Matalauta da mabukata suna neman ruwa, amma babu kome; harsunansu sun bushe saboda ƙishi. Amma Ni Ubangiji zan amsa musu; Ni, Allah na Isra’ila, ba zan yashe su ba.
18 I will open rivers in the high hills, and fountains in the midst of the plains. I will turn the desert into pools of water, and the impassable land into streams of water.
Zan sa koguna su malalo a ƙeƙasassun tuddai, maɓulɓulan ruwa kuma a kwaruruka. Zan mai da hamada tafkunan ruwa, busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓulɓulan ruwa.
19 I will plant the cedar in a deserted place, with the thorn, and the myrtle, and the olive tree. In the desert, I will plant the pine, and the elm, and the box tree together,
Zan sa a hamada ta tsiro da al’ul da itacen ƙirya, da itacen ci-zaƙi, da zaitun. Zan sa itace mai girma a ƙasashe masu sanyi ya tsiro a ƙeƙasasshiyar ƙasa, tare da fir da kuma saifires,
20 so that they may see and know, acknowledge and understand, together, that the hand of the Lord has accomplished this, and that the Holy One of Israel has created it.
don mutane su gani su kuma sani, su lura su kuma fahimci, cewa hannun Ubangiji ne ya aikata haka, cewa Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya sa abin ya faru.
21 Bring your case forward, says the Lord. Bring it here, if you have anything to allege, says the King of Jacob.
“Ka gabatar da damuwarka,” in ji Ubangiji. “Ka kawo gardandaminka,” in ji Sarki na Yaƙub.
22 Let them approach and announce to us the things that will occur. Announce to us the things that were before. And we will apply our heart to them, and we will know their end. And so, reveal to us the things that will occur.
“Ka shigar da gumakanka don su faɗa mana abin da zai faru. Faɗa mana abubuwan da suka riga suka faru, domin mu lura da su mu kuma san abin da zai faru a ƙarshe. Ko kuwa ku furta mana abubuwan da za su faru,
23 Announce the things that will occur in the future, and we will know that you are gods. Likewise, accomplish good or evil, if you are able, and let us speak of it and see it together.
faɗa mana abin da nan gaba ta ƙunsa, don mu san cewa ku alloli ne. Ku yi wani abu, mai kyau ko mummuna, don mu ji tsoro da fargaba.
24 Behold, you exist out of nothing, and your work is from what does not exist; he who has chosen you is an abomination.
Amma ku ba kome ba ne kuma ayyukanku banza da wofi ne; duk wanda ya zaɓe ku abin ƙyama ne.
25 I have raised up one from the north, and he will arrive from the rising of the sun. He will call upon my name, and he will reduce magistrates to mud, like a potter working with clay.
“Na zuga wani daga arewa, ya kuwa zo, wani daga inda rana ke fitowa wanda yake kira bisa sunana. Yana takawa a kan masu mulki kamar da taɓarya, sai ka ce maginin tukwane yana taka laka.
26 Who has announced this from its rising, so that we may know it, or from its beginning, so that we may say, “You are just.” There is no one who either announces, or predicts, or hears your words.
Wa ya faɗi wannan tun daga farko, don mu sani, ko kafin ya faru, don mu ce, ‘Ya faɗi daidai’? Ba wanda ya faɗa wannan, ba wanda ya riga faɗe shi, ba wanda ya ji wata magana daga gare ku.
27 The first one will say to Zion: “Behold, they are here,” and to Jerusalem, “I will present an evangelist.”
Ni ne na farkon da ya ce wa Sihiyona, ‘Duba, ga su nan!’ Na ba wa Urushalima saƙon labari mai daɗi.
28 And I saw, and there was no one among any of them to consult, or who, when I asked, could answer a word.
Na duba amma ba kowa ba wani a cikinsu da zai ba da shawara, ba wani da zai ba da amsa sa’ad da na tambaye su.
29 Behold, they are all unjust, and their works are empty. Their idols are wind and emptiness.
Duba, dukansu masu ƙarya ne! Ayyukansu ba su da riba; siffofinsu iska ne kawai da ruɗami.

< Isaiah 41 >